UKU-BALA'I 20

UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​WÉ› ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucÉ‘tÉ›, MѳtiѵɑtÉ› ɑɳɗ ɛɳtɛʀtÉ‘iɳ ѳuÊ€ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA ASHIRIN.
Dubansa take yi da wani irin yanayi na na raina wayonka da azanicin ka kafun ta kau da kai tana mai sakin guntun tsaki ta nisa cikin yanayi na haushi.
"Ban san mai ya hau kan ba Dr.Erena sosai ka bani mamaki ban taba zaton kalaman nan za su iya fitowa É—aga bakin ka ba ka dube ni up zuwa down ban yi maka kama da mai karamin tunani irin naka ba aiki na zo yi a wannan company ba zaman zance mara kan gado ba".
Ta karashe tana mikewa kan kafafuwanta fuskar dauke da tsananin bacin rai sai dai kuma acan kasar ruhinta da zuciyarta ba haka bane domin kuwa murna take har da tsalle-tsalle Dr.Erena ya kusan fadowa komarta abin da ta jima tana KUDIRI da muradin tabbatarsa kenan.
"Areef..".
Da sauri ta daga masa hannu kafun ta dauki jakarta dake ajje kan table din Office din nasa.
"Ya isa haka bana bukata ban so ka takura min, in kuma kace takura min zakayi wallahi yanzun nan zan rubuta maka takardar ajje aiki...".
Da sauri ya mike jin abin da take fadi jikinsa har É“ari yake yi ya iso inda take tsaye ya kafeta da idanunsa da suka gama tafiya a duniyar Areefa.
"No Please ba sai mun je wannan matakin ba...But Areefa ya kamata ki fahimce ni mana alkawari nayi miki komai kike so kuma ko me kike so ayi na miki alkawari...".
Da sauri ta watsa masa wani kallo wanda yake kara rikita masa lissafi kafun ta tsume fuska.
"Ban san ta ya zan maka bayani ka fuskanta ba Dr.Erena ban san da wani irin kalami zan yi amfani ka gane abin da nake nufi ba".
Tana gama fadin haka ta fara taka kafafun ta ta doshi kofar fita zuciyarta cike da abubuwa masu matukar yawa.
Shi kuwa shanye baki yayi yana kallonta har ta fice kafun ya ajje wani numfashi mai karfi ya koma ya zube kan daya daga kujerun Office din nasa.
******
*FIRST CLASS INTERNATIONAL SCHOOL GWADA*
Sosai farinciki ke wanzuwa a fuskarta tun lokacin da Dr.Karami ya danko ta daga gida zuwa haÉ—aÉ—É—iyar makarantar da ya zaba mata zata cigaba da karatun ta.
Zaune take zuciyarta falla da farinciki mara musaltuwa har da guntayen hawayen na farinciki duban Dr.Karami take cikin wani irin yanayi wanda ita kanta ta kasa tantacce matsayin da take ji ya samu a zuciyarta sosai take jin matsayi mai girma game dashi a filin zuciyarta sosai take jin komai na canzawa a duniyar rayuwarta a yau daya kadai sosai take hango mafarkinta zai tabbata na son karatu da ta jima tana rokon Allah ya bata damar da za tayi shi yau gashi Allah ya jeho mata Dr.Ƙarami mutumin da bata taba zaton za ta gan shi a duniyar mafarkin ta ba balle a zahiri amma gashi Allah ya kawo matashi ta hanyar da bata yi zato ko tsammani ba.
Numfashi ta ja kafun ta dago kai ta na kallon Office din da ta baro shi a ciki shi da shugaban makarantar suna zantawa.
Kamar daga sama taji an dafa mata kafaÉ—a da sauri ta dawo daga duniyar tunanin da ta fada dago kanta tayi ta sauke kan wata matashiyar yarinya wacce a shekaru za suyi kai daya sai faman murmushi take sakar mata cikin yake ita ma Mariya ta sakar mata da martani.
"Sannu ko sunana Baseera Haruna Sa'eed ni sabuwar daliba ce da Dadyna ya kawoni yau ke ya sunanki".
Mariya da ta saki baki da idanuwa ta na kallon ikon Allah sai yanzu ta kyafta idanu kafun ta sake murmushi tana motsa laɓɓanta cikin mamaki da wannan kanzagi da zalaka na wannan yarinyar sai kace ta tambaye ta saki baki sai ratata zance take yi kamar an kunna rediyo ana sauraron shirin INDA RANKA.
"Karki damu haka nake shi kansa Dadyna aku yake ce mani wai na fiye surutu shiyasa yace kawai nafi dacewa na zama yar jarida".
'Kuma dai!'
Mariya ta fadi a zuciya tana tallaɓe haɓa kafun ta nisa.
"yo ai ni kin hanani ma cewa komai sai zuba kike yi dole dadynki yace dake Aku ke ba ki san ni ba nima ban sanki ba amma kin saki baki sai watso mani zancen ki ke kamar na tambaye ki".
Da sauri ta caɓe.
"Woohh ai na san ke ba mai cutar wa bace daga ganinki kina da kirki da natsuwa sosai da sosai domin dady yace in zan yi abokiya na samu mai natsuwa ba irina mai shegen surutu ba".
Dariya sosai Mariya take yi har tana rufe bakin ta mamaki take yi da halin Baseera sosai da sosai taji lokaci guda taji ta kwanta mata rai.
"to ni dai zancen ya tsaya nan naji abin da Dadynki yace yanzu dai ke a ina kike kuma aji nawa kike...".
yarfar da hannu tayi tana mai yatsine fuska.
"wai fa ss-1 nake daga makarantar da muka baro da yake dadyna ma'aikaci ne sai aƙayi masa canji aka kawo sa nan garin shine zai canza min makaranta wai sai dai a mai dani js-3 ki ji fa don Allah ai wannan ci baya ne kamar ni kuma fa ina da kokari sosai da sosai...".
"Yaa Allah! Baseera wai don Allah bakin ki baya ciwo ne don Allah tsaya ki ja numfashi mana".
Mariya ta tare ta tana mai kama hannunta ta na zaunar wa kan kujerar da take zaune a kai.
"karki damu akan haka nima yanzu placement zan rubutu na tafi ss-1 kin ga kawai sai mu tafi tare...".
Wata irin zabura tayi tana dariya.
"da gaske ki ke don Allah to shikenan ma na hakura da fa balli na tayar nace ban yarda ba amma tun da kin ce haka zan zauna saboda ke my abokiya".
"Yaa Allah Baseera Oh My God wai ke don Allah yaushe zaki yi hankali ne Yaa Allah!".
Wata murya ce suka ji kamar daga sama tana fadin haka da sauri Baseera ta zabura tana dosar mutumin da yake tsaye nesa dasu hannayensa sarke a kirjinsa sai faman kallon su yake yi da yanayi na damuwa a fuskarsa.
"dadyna zo ka ga my new ƙawa wallahi mai kyau da ita ga ta da natsuwa irin ƙawar da kace nayi...".
Janyo ta yayi yana jan kunnan ta wata karamar kara ta saki.
"Dady Please don Allah ba zan sake ba".
"Ban san yaushe zaki girma ba Baseera ke ko gajiya ba kya yi da surutu haba mana! a ko ina sai kin nuna halin ki nikam zan ce ma na fasa saka ki a makarantar ba zan iya da rawar kan ki ba...".
"wayyo Allah dadyna Please for give me I'll never do that again".
Yanayin da ta marare ce taka langwashe murya ya sanya shi dungure mata kai yana murmushi halin Baseera sai ita duk yarda ta san zai sanya ka ki daukar hukunci akan ta ta sani.
"Zo mije ka ga my New Ƙawa please dadyna".
ta fadi tana jan hannunsa shi kuwa sai fizgewa yake yu amma taki dai nawa har sai da ya bi ta sannan ta daina magiya har zuwa lokaci Mariya na zaune idanuwanta akan su duk abin da suke yi tana kallo wani burgewa da sha'awa suke mata sosai da sosai taji Baseera da mahaifinta sun burgeta yarda suke kulawa da juna da nuna soyayya tausayin kanta take tana tuno nata mahaifin in da yana nan da shi ma haka zai nuna mata soyayya fiye ma da ta Baseera amma ina! hakan ya gagara ƙaddara ta rabata dashi rabuwar da ba ta san a wani hali yake ba ba ta san yaushe ne zai dawo duniyarsu ba su cigaba da rayuwa a tare a inuwa daya.
Tsiwar Baseera ce ta dawo da ita duniyar zahirin ta daga ta tunani nisawa tayi taja murmushi kafun ta dubi mahaifin Baseera da yake tsaya yana dubanta.
"Ina yini dady".
Mariya ta fadi cikin muryarta mai sanyi da girmamawa a ciki.
Sosai yaji ta burgeshi sosai yaji yana so su kulla ƙawance da yarsa ya lura akwai natsuwa da hankali a tattare da ita.
"lafiya yau ya hakuri da aku mai bakin magana".
Murmushi ta saki don ta fahimci in da ya dosa da maganar sa kasa tayi da kai tana mai amsa masa.
"Dadyna ka ga ba ta fada min sunanta ba amma ni na fada mata".
Baseera ta fadi tana mai duban Mariya da take kallonta fuskarta dauke da murmushi.
"Yaa Allah! ta ya ya za ta fada miki bayan kin cika mata kunne da surutu Allah yasa ma tace ba za tayi kawancen ba...".
"Dadyyy!".
Baseera ta fadi da rigima a muryarta kamar zata fashe da kuka duban Mariya tayi cikin yanayi na mararecewa.
"Please don Allah fada min sunanki kin ji in ba haka ba nace ba zan yi makarantar ba ma".
Yanayin da tayi maganar da gaske take hakan ya baiwa Mariya dariya ganin da gaske take.
"sunana Mariya Bello Gwada".
"woohh so Fastastic Nice Name".
Baseera ta fadi tana mai kambama sunan Mariya.
Ya tsine fuska Mariya tayi kamar wacce aka tsikarawa allura da sauri Baseera ta ware idanu alamun tsoro tashiga tambayar ta lafiya mai ke damunta?.
Girgiza kai tayi alamun bakomai amma ita kadai ta san abin da take ji tun da ta tashi yau take jin wani iri a jikinta kamar bata da lafiya lokaci-lokaci take jin cikin ta da mararta na murɗa mata sai taji kamar numfashinta zai dauke amma ba wanda ta fadawa haka sai dauriya da take yi taki bari kowa ya gane sai dai in ya motsa mata take cizon laɓɓanta har ya lafa.
Miƙewa tayi jin mararta ta daure sosai tana faman cizon laɓɓanta sosai Baseera ta lura da haka da sauri tayi wa mahaifinta nuni da abin da Mariya take yi da sauri shima ya ware idanuwansa sosai akan ta kafun ya dafa kafadarta.
"lafiya Mariya me ke damun ki ko baki da lafiya ne?".
haÉ—e jikinta tayi waje daya ji take yi kamar kayan cikin ta za su zubo kasa da sauri ta durkushe kasa tana mai sakin numfashi da sauri-sauri hakan da Alhaji Haruna ya gani ya sanya shi firgita kadan da sauri ya kamo ta sosai yana mai duddubata Baseera dake tsaye kuwa jikinta sai faman É“ari yake yi idanuwanta lokaci guda suka kaÉ—a sukayi jajir.
"Dady what is wrong?".
Muryarta a raunane kamar mai son fashewa da kuka.
"Mariyaaa!".
Muryar Dr.Karami da karaÉ—e wajan lokacin da ya fito daga office idanuwansa suka gane masa abin da ya sanya shi faduwar gaba idanuwansa a warwaje da sauri yayi jifa da ledar dake hannunsa ya tako cikin sassarfa kamo ta yayi sosai izuwa lokacin har ta fara ficewa daga hayyacinta hakan da ya gani ya kara tsora tashi da sauri ya dubi su Baseera da Mahaifinta cikin yanayi na tuhuma kafun ya kau da kansa cak! ya dauke ta yayi hanyar ficewa da ita daga wajan hakan da suka gani su ma sai suka rufa masa baya wajan da yayi Parking ya isa ya buÉ—e gidan baya ya sakata ya rufe kafun ya dawo gaba ya shige duk abin da yake yi cikin yanayi na tsoro da fargabar abin da zai je ya dawo key yayi mata kafun ya fizgeta ya bar harabar wajan suma Su Baseera motarsu suka hau suka rufa masa baya.
Wani clinic ya nufa da ita dake kusa da makarantar cikin sauri yayi parking ya zo ya sungume ta yayi ciki da ita ba wani bata lokaci aka amshe ta kayi emergency da ita sosai Dr.Karami ya shiga tashin hankali ba abin da yake tsoro illa wani abu ya samu Mariya bai san abin da zai ce da iyayenta ba bai san da wani ido zai kalle su ba bai san a me za su dauke shi ba fata yake yi Allah ya saukaka lamarin Allah yasa ba wani abu ne ya same ta ba.
Kafadarsa yaji an dafa hakan ya san yashi tsayawa cak! daga Safah da Marwa da yake faman yi a kofar dakin da aka shigar da Mariya da sauri ya juye ya dube shi shima shi yake kallo kafun ya kau da kai bai san shi ba bai ma taba ganinsa ba amma sosai zuciyarsa ke nazarin mutumin domin kuwa abun da yafaru da Mariya a wajan su ne yana zargin su komai ya faru da ita su ne sila numfashi yaja kafun ya sake dubansa.
"Mene ne hadinku da Mariya mai kuka mata?".
Abin da ya fadi kenan muryarsa da zurfi a cikinta yana faman haÉ—e fuska waje daya.
Sosai Alhaji Haruna yayi murmushi kafun ya bugi kafadar Dr.karami kadan.
"Haba mana abokina karka zarge mu da komai a kan yar uwarka ba abin da muka yi mata...".
"Ta ya kake so na yarda da maganarka...".
Kafun ya dire ya jiyo muryar Baseera cikin kuka tana cewa 'Ina Mariya?'.
Mamaki ne sosai ya cika sa ya shiga duban Baseera da alamun tambayoyi masu yawo sosai yake kallonta ko zai gane fuskarta amma ina bai ga alamun sanayya ba a tattare da ita kuma bai san taba balle yace yar uwar Mariya ce.
"ya kamata ka fahimci wani abu a kan Baseera ba mu da niyyar cutar da ita kamar yarda ka ganmu a yau mu ma haka a yau mu ka fara ganin ka Baseera Da Mariya cikin wannan lokaci suka hadu na kawo Baseera zan saka ta a wannan makarantar to a nan ta gano Mariya har take cewa dani tayi ƙawa shine fa na zo ganinta har mun gaisa ma sai naga ta shiga wannan halin Dan'uwa karka zargemu da komai wallahi zuciya daya muke tare da ku ba mu da niyyar cutarwa gareku don nasan illar haka".
Tun da ya fara magana Dr.Karami ke dubansa da idanunsa sosai ya fuskanci gaskiya a cikin kalaman sa sosai ya gane mutum ne mai kamal da hankali gami da natsuwa lokaci guda yaji kunyar abin da yayi domin kuwa Alhaji Haruna zai girme masa nesa ba kusa ba.
Murmushi yayi yana sosa keya kafun ya dubi Alhaji Haruna.
"Afuwan na tuhume ku akan abin da ban san ya yake ba kuyi hakuri Mariya amana ce a waje na dole in shiga yanayi in na ganta cikin wani hali".
"kana da gaskiya hakan yayi daidai yanzu dai wani hali take ciki".
GÆ´aÉ—a kai yayi kafun ya nisa.
"sun shigar da ita ciki domin dubata...".
Bai kai ga karasawa ba likitan da ya shiga duba Mariya ya fito yana duban su kafun ya ba su hannun suyi musabaha yana mai duban su daya bayan daya har ya dire kallon sa ga Alhaji Haruna.
"Kai ne mahaifinta ko?".
Ya tambaya kafun ya dora.
"karka damu tana lafiya lokacin ta ne yayi nasu na mata kuma bata saba ba shiyasa ta shiga wannan hali amma Alhamdulillah muyi settling din komai yanzu haka ta samu barci nan da 30mint komai zai zama normal".
Hamdala sukayi su duka kafun Alhaji Haruna ya nisa.
"Muna godiya Doctor sosai da sosai Allah ya bata lafiya".
"Ameen.Yanzu dai zan muku last na magungunar da za a sai mata tana amfani dashi".
GyaÉ—a kai sukayi Dr.Karami shi dai shiru yayi yana mamaki yarda Alhaji Haruna ya zage yana nuna shine Mahaifi gareta ba tare da nuna eh da gaske ba 'yar sa ba ne hakan yayi masa dadi a rai lokaci guda yaji mutumin na burgeshi sosai da sosai.
Ko da ya dawo daga duniyar tunani mamaki ne ya sake kashe shi ganin Alhaji Haruna yabi likita Office din sa sakato yayi da baki ya duban hanya kafun ya dawo da kallon sa wajan Baseera da ta zauna ta zabga tagumi hannu bibbiyu kamar wacce aka aikowa da mutuwar wani a dangin su duk bakin surutu ya mutu kamar ba ita ba ce aku a dazu.
"Ya sunanki?".
Dr.Karami ya fadi yana mai duban ta cikin yanayi na mamakin yanayin da ya ganta aciki kuma ya san duk a dalilin Mariya ne.
Ba ta an sashi ba illa kallo da ta yi masa tana mai sauke numfashi mai kwari sosai.
"C'mon Baby girl tell me your name...ko ba kya so ƙawancen da Mariya ne".
Ba tayi niyyar ansa shi ba amma jin abin da yace ya sanya ta sauri dubansa da murmushin yake.
"Please don Allah karka hana Mariya ƙawance dani sosai nake son ta a raina a lokaci guda naji ta burgeni kuma Dadyna ya na son ta ya yaba da hankalinta sosai da sosai".
"Oya C'mon tell Now".
Murmushi ta saki ganin yarda yayi mata cikin yanayi na wasa.
"Baseera Haruna Sa'eed".
Sosai yake dubanta yana tunanin in da ya san sunan mahaifinta sosai yake zaton ya san sunan amma ya manta a ina ne ya san haka gyaÉ—a kai yayi kafun ya nisa fuskarsa da murmushi.
"Masha Allah to naji na amince kuyi ƙawance But...akwai sharaɗi kafun amincewar...".
"Na yarda wallahi tell me".
Ta fadi cikin yanayi na zagwadi dubanta yake yi sosai, sosai ya lura i Baseera irin mutanan nan ne masu barkwanci da wasa da dariya a ko ina suke.
"ban da wasa in an fara karatu ina so ku hada kan ku waje gudu sosai nake so naji ana alfahari da ku a cikin makarantar nan".
"Promise".
Ta fadi tana mai dariya burin ta ya cika na samun ƙawa a lokaci daya daga zuwa makaranta.
"hala tana nan tana yi maka halin nata na surutu kamar aku".
Muryar Alhaji Haruna ta yanke musu hirar tasu Murmushi Dr.Karami yayi kafun ya dubi Baseera da ta cuno baki gaba alamun ba ta so abin da dady yayi mata ba.
"Yaa Allah! Ai ba za tayi ba tayi mani alkawari dainawa in kuma ta cigaba ba zan barta ta cigaba da ƙawance da Mariya ba".
"yawwa kayi mani daidai".
"kai dady".
Baseera ta fadi fuska a shagwaɓe har sai da ta basu dariya su duka.
"ku tashi mu shiga mu duba ta ko?".
Ya fadi yana mai dubansu ai kamar jira take cikin hanzari ta mike tayi hanyar shiga dakin har tana kokarin buge Dr.Ƙarami shi kam dariya abin ya bashi shikuwa dady dafe kai yayi kawai yana mai duban Dr.Karami yana mai masa nuna da ido yayi hakuri ba ta da hankali murmushi kawai ya yi yayi gaba.
Kwance suka tadda ita sai faman sharar barci take yi kallo daya zakayi mata ka gane ta ji jiki a dan lokacin don har fuskarta ta fada sosai Dr.karami yaji wani iri a ransa ganin yanayin da Mariya take ciki ji yake yi kamar ciwon da yake jikinta ya dauko ya mai doshi nashi jikin bai son abin da zai sake taba mata rayuwa bai son abu ko ya yake ya rikita Mariya sosai yake jin tausayin ta sosai yake jin wani iri game da ita duk lokacin da take cikin hali na damuwa sosai yayi KUDIRI a zuciyarsa da ruhinsa da izinin Allah sai ya canza mata rayuwa sai ta ji dadin rayuwa sai taji dadin yan uwa sai ya zame mata yan uwan da take kwadayi a rayuwarta sai yayi iya kokarin sa don ganin ta fuskanci rayuwar 'yanci duk wani kunci da damuwa sun bar duniyar ta sai dai bai san ta yaya zai yi wannan aikin ba bai san wacce hanya bace da zai bi amma dai zai yi iya bakin kokarin sa don ganin rayuwar Mariya ta zama normal like others.
Sai da suka shafe awa daya kafun Mariya ta farko sosai da sosai take duban su da idanuwanta da suke bude runtse idanu tayi ta shiga tunano abin da ya faru da ita wasu hawaye suka zubo mata a hankali ta ja numfashi kafun ta buÉ—e idanunwanta Baseera ta gani kusa da ita ta mai sakin mata murmushi ta sanya hannu ta dauke mata hawayen da suke zubo mata.
"Sannu ƙawata".
Ta fadi cikin yanayi na taushin murya da jajantawa.
Ba ta ansa ba sai duban Dr.karami da tayi da ya tallaɓe haɓa ya zuba mata manyan idanuwansa masu firgita mata tunani gyaɗa kai tayi tana masa kallon tambayar me ke faruwa mai ya kawo ni nan?.
Sosai ya gane abin da take nufi amma sai ya kau da kai domin bashi da bakin da zai iya cewa ga abin da ke faruwa da ita so yake yi sai sun koma gida komai a natse sannan sai suyi magana sosai da sosai.
"ina ke miki ciwo Mariya?".
Alhaji Haruna ya fadi cikin yanayi na tausayawa gyaÉ—a kai tayi alamun babu.
"Masha Allah haka ake so Allah ya kara lafiya ko Mariya"
GyaÉ—a kai ta yi kawai sosai take hango karamin ci irin na wadannan mutanan daga haduwa amma sun yi mata abun da wasu nata suka gagara yi mata sun bata kulawa da duk lokacin su sun tausaya mata da halin da ta shiga sosai taji sun samu matsayi mai girma a zuciyarta sosai take hango martaba da karamci tattare da su bata da bakin da zata ce da su komai sai fatan alheri.
Ba su jima cikin asibitin ba bayan dube dube da likita ya sake yi mata ya tabbatar da ba komai ya ba su sallama domin tafiya gida a tare suka fita Baseera da Dady su ka hau mota daya ba don ta so ba don cewa tayi sai dai ta bi Mariya gidan su amma Dady yace tayi hakuri zai kai ta da kan sa zuwa da yamma suna cikin wannan yanayin ne Mariya dake tsaye jingine da motar Dr.karami tana kallon diramar da ake yi da Baseera sosai taji wani abu a kafarta yana bin ta da sauri ta duba.
"Yaa Allah! Jini".
Ta fadi muryarta da karamin sauti da sauri ta dubi wajan da suke tsaye tana duban su a daidai lokacin Baseera ta dubeta ganin yarda tayi da ido ya sanya tambayar ta ko lafiya nuni tayi mata da kafarta da sauri ta iso gareta tana dubawa to da yake zata girmewa Mariya a shekaru sai ya kasance ta gane abin da ke faruwa kuma dama dazu taji abin da likita ya fadi da sauri ta dubi Dady da Dr.karami.
"Dady muje da ita gida don Allah She need help please dady".
Yanayin da tayi maganar sai ya sanya su duban Mariya da sauri don ba su gane akan me take magana ba.
Da idanu tayi musu nuni tsaf! Su ka gane ita dai Mariya kanta na kasa cikin hanzari suka shiga motar su suka dauki hanya da yake ba nisa gidansu Baseera tafiya kadan sukayi suka isa Babban gida ne kallo daya zaka yi masa ka gane mai shi yana da rufin asiri sosai da sosai get ne babba mai ruwan blue sai ratsin gold da kayi masa Horn daya sukayi aka buÉ—e musu gabadaya suka shige ciki bayan sun yi Parking duk suka firfito ita dai Mariya duk a tsora ce take sai faman haÉ—e jikinta waje daya take yi da sauri Baseera ta kama ta sukayi cikin gidan a falo su ka tadda Hajiya Abida mahaifiyar Baseera babbar mace ce mai cikar kamala da mutunci sosai ta dubi Baseera fuskarta da tuhuma.
"ba dai har kun dawo ba ina dadyn naki yake?".
Tana magana ta na duban Mariya da take haÉ—e jikinta kanta a kasa duban Baseera tayi da kallon karin bayani.
"later please Momy".
Ta fadi tana zarcewa da Mariya in da dakin ta yake suna shiga ta zarce da ita Toilet duk wani abun bukata sai da ta tadanar mata kafun ta nuna mata duk yarda zata yi sannan ta fito ta bar ta a Toilet din ma'ajiyar kayan ta ta nufa ta buɗe wata doguwar riga ta fiddo gami da wani hijabi mai kalar pink da ratsin kalloli daban daban wanda suka karawa hijabin kyau sosai bakin kafcecen gadon ta ta ajje su sanna ta zauna ta na mai zabga tagumi mintina goma Mariya ta shafe a toilat kafun ta fito tana raɓe-raɓe kamar mara gaskiya da sauri Baseera ta mike ta isa wajanta.
"dafatan kin yi yarda nace ko?".
GyaÉ—a mata kai tayi domin wata irin kunya ce taji ta lullubet sai sunne kai take yi kasa.
"Uhmm Karki damu kin ji ko Mariya ba abin da zai sa me ki in Allah ya yarda".
Kai kawai take gyaÉ—a mata a haka har ta su suke suka isa gida daidai kofar Gidan yayi Parking tsayuwar motar ne ya dawo da Mariya duniyarta da sauri ta dago kai dubi bangaren Dr.Karami da sauri tayi kasa da kai domin ita yake kallo a hankali ta sanya hannu ta buÉ—e kofar ta fice kamar daga sama idanuwanta suka hango mata abin da ya kusan sanyata sakin fitsari Huzaif ta hango zaune saman motarsa ya haÉ—e kansa da gwuiwarsa bisa alamu ya jima a wajan zaune da sauri ta juya ta dubi Dr.karami wani irin kallo ta ga yanayi mata mai cike da tuhuma sosai ta hango wani irin yanayi mai kama da bacin rai a fuskarsa kasa tayi da kai da sauri ta fara taka kafafunta wanda take jin su kamar za su narke sosai take jin kanta na wani irin juyawa kamar zai dare gida biyu duk taku daya in tayi sai ta ja numfashin ta da taji yana barazanar daukewa ba ta kai ga shig gida ba taji kugin tsayuwar mota da sauri ta juyo Dr.Aqeel ta hango yana fitowa daga ciki motarsa idanuwansa akan ta sosai ta firgita ganin wani kallo da shima yake yi mata wanda bata san da me zata fassara shi ba a ranta ta furta.
"Yaa Allah! me ke shirin faruwa da ni ne?".
Ai ba ta san lokacin da ta ja kafa tayi cikin gida ba sai faman haki take yi ba ta tsaya ko ina ba sai cikin dakin Umma ta baje kan katifar dake yashe cikin dakin sai faman sakin hirji take yi gabanta na faman bugu kamar zai tarwatse komai taji yana juya mata Umma da ke zaune ta shiga dubanta da mamaki da farko ba tayi zaton Mariya ba ce sai da ta kalleta sosai domin kayan da ke jikinta ba ta san ta da su ba tana kokarin yin magana ta tsinkayi sallamar Dr.Karami da sauri Mariya ta kara dunkulewa waje daya tana cusa kanta cikin hijabin dake jikinta gabanta na kara tsananta bugawa.
Ko ta kan ta bai bi ba Umma kawai yayi wa bayani abin da ya faru mamaki sosai taji nan ta shiga yi masa godiya amma shi ina hankalinsa na kan Mariya wani kallo yake watsa mata ta gefen ido kafun ya dubi Umma muryarsa da sanyi.
"Umma na mance shaf! in Allah ya kai mu gobe zan koma can wajan aikina domin hutun da na dauka ya kare ina muka fatan alheri sai na dawo".
yana gama fadin haka ya mike saman kafafuwansa Umma kuwa sai faman sheka masa addu'a take yi da neman tsari.
A haka ya fita ba tare da ya dubi Mariya ba baya ya ajje wa Umma bandir din kudi masu yawan gaske duk da zuciyarsa sai a zalzalar sa take yi
ita kam Mariya ba a maganarta domin lokacin da taji abin da ya fadi ba ta san lokacin da hawaye suka wanke mata fuska ba wasu katangun tashin hankali suka rikito mata akai lokaci guda taji wani zazzabi na shirin rufe ta gabadaya ta kasa motsi jikinta gabadaya taji ya canza kamar ba na ta ba komai taji ya sauya mata a kankani lokaci tsoronta daya Allah yasa ba fushi yayi da ita ba ya yanke mata wannan danyen hukuncin mai barazanar tafiya da numfashim ta kuka take yi na zuciya idanuwanta sai zubda hawaye suke yi sosai take hango tashin hankalin da za ta shiga in ba Dr.karami ta dade a wannan yanayin kafun wani mugun barci yayi awon gaba da ita ya je fata wata duniya mai dauke da Dr.Karami wanda ta kasa tantace ta mene ne sannan ta kasa gane wata irin rayuwa ce suke yi sosai ta hango tashin hankali mutane uku take hangowa ko wanne kuma ita ya dosa da abu mai girma wanda ta kasa gane mene ne?
*KAMALA MINNA*😘😘
Post a Comment (0)