YAWAITA SALATI GA MANZON ALLAAH A DAREN JUMA'A DA YININ JUMA'A

YAWAITA SALATI GA MANZON ALLAH ﷺ A DAREN JUMA'A DA YININ JUMA'A Yana daga cikin falalar Daren juma'a da yinin juma'a,Manzon Allah ﷺ ya umarnin mu yawaita yi masa salati a wannan lokuta,saboda Hadisin Anas bn Malik رضي الله عنه yana cewa:Manzon Allah ﷺ yace: (Ku yawaita yi mini. Salati a ranar juma'a da daren Juma'a,duk wanda yayi min salati guda daya,Allah zai yi masa salati guda goma) @صحيح الجامع DAGA CIKIN FALALA SALATI GA MANZON ALLAH ﷺ Wanda yayi Manzon Allah satai guda daya Allah zai yi masa salati guda goma @حسنه الألباني - الصحيحة 1407] Mafi kusanci da chanchanta ga Manzon Allah ﷺ a ranar alqiyama,sune masu yawaita yi masa salati @حسن لغيره - صحيح الترغيب1668 Manzon Allah ﷺ yana cewa,ku yawaita yi min salati, domin Allah ya wakilta wani Mala'ika na musamman a wajan Qabarina,babu wanda zaiyi min salati face wannan mala'ikan yace dani, wane dan wane yayi mata salati yanzu @حسنه الألباني الصحيحة 1530 Manzon Allah ﷺ wani mai zuwa ya zo min daga wajan Ubangijina,sai yace; Duk wanda yayi maka salati daga guda daya daga cikin al'ummarka,Allah zai rubuta masa kyakkyawan aiki guda goma,Kuma a kankare masa laifuka guda goma,kuma a daukaka Darajarsa sau goma,kuma a maida masa salatin shima ayi masa @صححه الألباني - صحيح الجامع | 57 ] Ku yawaita yi min salati ku jajirce cikin yawaita addu'a,kuma kuriqa cewa (اللهم صلِّ على محمد وعلى آل محمد، وبارك على محمد وآل محمد كما باركت على إبراهيم وآل إبراهيم إنك حميد مجيد) @صححه الألباني - صحيح الجامع | 3783 ] Wanda yayi salati guda daya,Allah zai yi masa salati goma @صححه الألباني - صحيح الجامع |6358] Babu wanda zaiyiwa Manzon Allah ﷺ Sallama,face Allah ya mayarmin da ruhina har sai na mayar masa da sallama @حسنه الألباني - صحيح أبي داود | 2041] Allah ne mafi sani Allah bamu ikon cika Umarnin Manzon Allah ﷺ da yawaita salati a gareshi.
Post a Comment (0)