MAIRO 10

♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*10*

Siraj dai sai kallonta yake can yaji bazai iya zurewa ba yace “wai mi kike yiwa kuka?”
cikin kukan tace
“ni gida nake so”
dariya yayi “gida?”
“eh”
“mi aka miki to?”
“bana son gidan nan bana son gida a sama kuma mumi faɗa take min”
fashewa sukayi da dariya Nura yace “hala baki taɓa ganin gidan sama ba?”
“eh nidai bana sansa”
tashi nura yayi yana faɗin “amman gaskiya kauyancinki yayi yawa”
k'ara turo baki tayi kuka nason fito mata fili Siraj dai kallonta kawai yake har ya kare cin abinci ya tashi,

Mairo tasowa tayi ta dawo kusa da doguwar kujera dake parlour ta zauna har lokacin hawaye take.
jin tafiyar momi yasa ta ɗago kai tana kallon up stairs “lafiya kike kuka?”
fuskar momi a haɗe take mata tambayar
“gida nake so gurin Gwaggo”
murmushi momi tayi “karya kike yi ai ke kika dage saikin biyomu jiya jiya muxo yau kice a kaiki gida babu yadda bayiba akan ki zauna kika ki”
hannayenta ta haɗe tana rokon momi
“na daina mumi bazan sake cewa a zo dani ba”
“uhmm tashi muje kicin kiyi wanke wanke”
lake kafaɗa tayi “ni ban iya wanke wanke ba”
kunneta momi ta kamo “ke bari kiji na faɗa miki iskancin da kike can kauye nan bazaki min shiba”
kuka Mairo tasa sai kiran Gwaggo take.

haka momi taja hannunta suka nufi kicin.
gurin wankewanke momi ta nuna mata ta “oya sa hannu ki wanke” kallon momi tayi idonta cike da hawaye tace “wlh ban iya wanke wanke ba”
“dukanki dai kikeso nayi kamar zakice baki iya wanke wanke ba kuma rikon kauye ba birnin ba koki wanke shi ko na miki dukan tsiya” momi na kaiwa nan ta juya tabar kicin ɗin,

haka Mairo ta hau wankewanke tana kuka
sama take wankewa dan har ga Allah bata iya ba tunda Gwaggo bata sata aikin komai inba sharaba koshi inta ga damane take yi.
haka ta wankesu samasama kofukan da akasha tea ma ɗaurayisu kawai tayi ta aje,
koda ta kare ta fashe tea cup ɗaya kuma duk ta ɓata gurin da ruwa ɗan kwalinta tasa ta goge ruwan ta jefashi bayan firjin.
jikinta a sanyaye ta nufo parlour tsaye tayi tana kallon momi dake zaune saman kujera.
ganin bata kula taba yasa ta karaso kusa da ita “na kare”
sai lokacin momi ta kalleta “to wuce kiyi wanka”
“ina?”
“inda kika ga na miki jiya”
lake kafaɗa tayi tayi baya baya “ni bazan hau sama ba gaskiya”
taɓe baki Momi tayi ta cigaba da kallon tv.

*****
ranar Mairo wuni tayi tana kuka saboda faɗan da momi tayi mata kuma ta hana mata abincin rana saboda takiyin wanka.

da magariba Mairo na gefen kujera zaune Momi ta nufi kofa da sauri Mairo ta tareta tana “ni ki bani abincina yunwa nake ji”
tureta momi tayi saida ta faɗi wani mahaukacin ihu ta saki momi saida ta rufe kunnuwanta ta hau shurenta.
“lafiya?”
Qasin na shigowa abunda ya fara tambaya kenan

momi ta nunata da yatsa “rainin wayo ne da ita so nake na gyara mata zama”
karasawa yayi ya tada ta “mi tayi momi?”
“iskancin da take can kauye ne take son tamun”
kallon Mairo yayi “mi kika mata?”
cikin kuka Mairo tace “ban mata komai ba muguwace azzaluma ƙk'atuwar banza kuma ban yafe miki b-”
da sauri Qasin ya rufe mata baki “ke karna sake ji ba mamanki bace”
kai ta girgiza tana hawaye “ni ban sonta ba mamana bace”
kwafa momi tayi “aiko kashinki ya bushe cikin gidan nan”
“wai minene mafarin wannan abun ne momi?”
momi tace “rantsuwa nayi duk batayi wanka ba bazan bata abinci ba”
kallon Mairo yayi “ke mi ya hana miki wanka maryam kin fi son ki zaina da k'azanta?”
“a a itace tace saina hau saman sama sannan nayi wanka ni kuma tsoro nake ji”
kallon momi yayi yana murmushi “kinji momi tsoro take ji kinsan ko ɗaxun saida aka saukarda ita”
“ba wani tsoro iskancine kawai”
“ba iskanci bane ko?”
ya tambayi Mairo kai ta ɗaga yace “bata hakuri sai kuje tayi miki wanka kuma karki kara rashin kunya kinji”
saida ta daɗe sannan ta kalli momi kasa2 tace “yi hakuri bazan sake ba”
da ita da dashi duk tsurawa momi ido sukayi sunajiran abunda zatace

saida ta watsa masu harara sannan ta fixgi hannun Mairo suka nufi up stairs.
kankame momi Mairo tayi ta rumtse ido nan momi ta sakar mata hannu “wuce da kanki”
kuka tasa nan momi ta katsa Mata tsawa dole ta rike karfen ta rika hawa da rumtsen ido har ta haye.
momi ce tayi mata wanka Mairo kan ana mata wanka tana tunanin yadda za ayi ta tsera ta gudu ta bar gida,
bayan sun fito momi ta wulgo mara kayanta ta sauka downstairs ta ɗebo mata abinci.

*_washe gari....._*
tun asuba momi ta tada Mairo bayan sunyi sallah bata barta ta koma bachi ba suka nufi kicin.
tare suka haɗa komai na breakfast ranar momi batayi mata faɗa ba dan tare sukayi komai duk da ba wani iyawa tayi ba daman momi abunda bata so ta saka aiki kaki da kuma kuka.

*_8:30am....._*
suka kare hada komai momi ta nunawa Mairo gurin da zata jera.
ba musu ta rika jera abinci badan ranta yaso ba sai dan gudun matsifar momi aranta kan ɗebima momi albarka kawai take tana aiban ta'ta.
Mairo ce ta fara zama bayan ta jere breakfast ɗin sannan momi,
Usman da Nura dake zaune saman kukera suka nufo dining.
Siraj sai janta yake ita kuma ta wani haɗe fuska kamar ta fasa kuka .
momi da kanta ta zubawa Mairo breakfast su kuma suka shiga zubawa kansu.
Nura ya kalli Momi yace “yau yaya ba zai karya nanba ?”
momi tana k'ok'arin zuba ma kanta tace “zaizo mana ai kasan nan yake karyawa kila bai tashi bachi bane”

kamar daga sama sukaji an banko kofar parlour duk juyawa sukayi suna kallon Qasin daya shigo fuska a haɗe.
yana karasowa momi tace “lafiya?”
takardun dake hannunsa ya nunawa momi cikin zafin rai yace “kwangila ce Yarima yakai a kanfaninmu”
murmushi momi tayi “wow...-”
tare numfashinta yayi ya juyarda fuska “haba momi kamar bakisan Yarima ba he just want to ruin my life kuma deal ne between me and him saina gani tsakanin ni da shi who is going to be loser”
tashi momi tayi ta daga hannunta da niyar yi masa magana sai kuma ta kasa jefarda takardun yayi ya fice cike da bacin rai.

*HAPPY JUMMA'AT MUBARAK.*
_i Really Need Your Prayers fans Ina Ciyon Zuciya_

© *Khadeeja Candy*

Post a Comment (0)