♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*11*
sanyi jikin momi yayi ta kasa kai komi bakinta Nura da Usman ne kawai suke cin abinci shima Siraj ya damu sai kallon momi yake,
tashi momi tayi ta nufi gurin daya watsarda takardun ta shiga haɗawa.
saida ta haɗesu guri ɗaya sannan ta kalli Siraj daya juyo yana kallonta tace “Siraj jeka kiran min yayanku”
kai kawai ya ɗaga mata ya tashi ya fice.
Mairo dai sai satar kallonsu take tana tsomen beredi,
guri momi ta samu ta zauna dafe da kai kamar mai mata ciyo.
tana haka Qasin da Siraj suka shigo dining Siraj ya nufa Qasin kuma ya nufota yana faɗin “gani momi”
kujera momi ta nuna masa har lokacin tana ɗafe da kai.
bayan ya zauna ta kalleshi tace “Qasin ka rika hakuri kasan da wadda kake zama Qasin ni bana tunanin saboda ɓata maka suna ko karyarda kai Yarima ya ɗauki kwangila ya baka”
kawar da kai yayi alamar bai jidaɗin maganar ba.
ganin haka yasa momi ta taso ta dawo kusa dashi ta zauna “Qasin ni a ganina kamar ma Yarima yana son ɗaukaka kanfaninku ne”
juyowa yayi ya kalleta “a a momi so yake ya karya ni kawai kuma bazan taɓa yarda da wannan kwagilar ba ba zai taɓa cinma burinsa a kaina ba”
dafashi momi tayi “ban sanka da zuciya haka ba bana son ka runtse ido ka yanke hukuncin da zai zamar maka nadama nafison ka yanke hukunci ido a buɗe
bana son abunda zai saka cikin matsala Qasin”
kallon momi yayi yana nazarin kalamanta can ya lumshe ido ya sauke ajiyar zuciya ya sake buɗe idon yace “momi banida mafita sai wannan momi bana son Yarima yayi nasara a kaina momi ki duba min plz”
itama Momi ajiyar zuciya ta sauke tace “baka ganin mayarda kwangilar zai zame maka matsala?”
“zai iya zama kan dan lokacin da zai bada kwangilar tare da yan jarida yazo”
“to karka kuskura ka mayarda kwangilar zai zubar muku da mutuncin kanfani”
“momi ba nida wata mafita sai wannan”
“haba Qasin sai kace kai ba namiji ba kai bakasan yadda zaka sarrafashiba ka bashi kunya ka taka abunda ya taka Qasin ka zama gawurtaccen namiji ba rago ba”
Siraj da tunda ake maganar hankalinsa na gurin tasowa yayi yana faɗin “yes yaya kaima namijine ka ya k'eshi ks kara ɗags martabar kanfaninka kabi shawarar momi plz”
ajiyar zuciya Qasin ya sauke a karo na uku ya kalli momi “momi ba hannuna da nasa ya bani kwangilar ba PA ɗina yaba kuma banida tambas dan zai iya haɗa kai dashi ya cutar dani”
Siraj yace “ka chanja PA kawai”
“haba Siraj how many PA I have to change just because of him? PA 4 na chanja akanshi bazan sake chanja wani ba not anymore”
cikin faɗa yake maganar jijiyar wuyansa na tashi da sauri Usman da Nura suka juyo suna kallon su, Mairo kara sakin baki tayi tana kallonsu daman hankalinta yana gurin,
dafashi momi tayi “ga wata shawara Qasin”
kai ya ɗaga mata ba tare daya kalletaba ‘uhmm’
“mi zai hana ka karɓi kwangilar kayi da kanka?”
murmushi yayi mai cike da jin haushi “haba momi ai zubarda kai ne daɗi zaiji na k'arɓi kwangila da hannuna masa”
“ba faɗuwa kayi ba Qasin cigabane a gareka da kuma ɗaga darajar kanfaninku”
kai ya girgiza “momi ba zaki gane ba”
“kaine baxa ka gane ba Qasin idan kayi haka mutane zasu yaɓeka suce bakada girman kai sannan kodan kwangilar tayi ya kamata kayi haka kuma idan tayi kyau zaka jawowa kanka customers ayaba maka ka kara samun ɗaukaka”
Siraj yace “gaskiya ne yaya ka ɗauki shawarar momi”
ya daɗe zaune gurin kamin ya ɗago kai ya kalleta “shi kenan momi zanyi yadda kikace”
murmushin jidaɗi Momi tayi ta shafa kansa “Allah ya maka albarka ya shige maka gaba”
shida Siraj suka amsa da ‘amin’
tashi yayi ya nufi kofa yana sauke ajiyar zuciya,
da gudu Mairo ta taso ta nufo shi tana faɗin “dan Allah ka je dani yawo inson fita”
fuska a haɗe ya shafa kanta yace “ba yanzu ba” ɓata fuska tayi idonta suka cika da hawaye shirinta na guduwa ya rushe .
juya tayi tana kallonsa har ya fice.
tashi momi tayi ta nufi up stairs tana faɗin “Maryam in kuka k'are ki haɗa kayan ki kai kicin ki wanke kuma ki share parlour nan ki goge”
kara ɓata fuska Mairo tayi abunda ta rsana kenan hawayen dake makale a idonta suka zubo.
© *Khadeeja Candy*