MAIRO 09

♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*9*

bayan Amimcewar Gwaggo saida akaje gurin tsoho tare da Mairo aka faɗa masa shima kin amincewa yayi saida yaga abun na Mairo bana wasa bane sannan ya yarda sosai Abbah ya jidaɗi daman tun rasuwar kanensa yaso a bashi ita Gwaggo ta hana,

sai goshin magariba (kusan magariba) suka kama hanya
so huɗu ana tsayawa Mairo nayin amai jikinta sai rawa sanyi yake nan da nan zazzaɓi ya rifeta saida aka kashe ac ɗin motar,

*_9:37pm....._*
suka isa Sokoto koda Qasin yayi farkin Mairo na rungume jikin momi tana bachi.
saida kowa ya fita sannan momi ta tasheta
a firgice ta fito motar tana ɗaga kanta hankes ya cika mata ido,
gidan sama ne mai hawa ɗaya ko ina an manna gulof murza ido Mairo ta shigayi dan gani take kamar mafarki take.

bayan momi ta fito Qasin ya rufe motar shida Mansura suka nufi part ɗinsu daman Abbah tuni ya wuce nashi part ɗin,

Mairo na tsaye tana kalle2 momi ta rik'a hannunta zasu shiga ciki Mairo tayi tsaye tana kallon kofar farlon da alama tsoro take ji,

faɗuwa gaban momi yayi tana tsoron kar kuma tace bazata shiga ba.
“lafiya zomu shiga ciki mana”
shiru Mairo tayi ta lakkafe kafaɗa
saida Momi ta maimaita sannan tace “nan ne gidan?”
“eh nan ne zo mu shiga ciki”
tsaye tayi kamar bazata shiga ba
momi bata bi ta kanta ba taja hannunta suka cigaba da tafiya.
jiki a sanyaye Mairo ta shiga farlon tayiwa hannun momi mugun rik'o Usman na kwance saman doguwar kujera yana bachi siraj kuma na kallo,

shine ya taso ya tari momi da far'ah “sannu da zuwa momi”

“yauwa sannu siraj baka kwanta ba?”

kayan dake hannunta ya k'arɓa yana faɗin “eh ban kwanta ba wacece wannan momi?”

kallon Mairo momi tayi “qanwarka ce”

“daga can aka zo da ita?”

“eh bari na shiga ciki”

Up stairs momi ta nufa Mairo na rik'e da  hannun Momi,
suna shiga bedroom Momi ta faɗi zaune saman bed ita da Mairo,
har lokacin tana  rike da hannunta

bayan sun ɗan huta Momi ta nunawa Mairo tawel “jeki ki ɗauki ga tawul can ki ɗaura sai kiyi wanka kici abinci ki kwanta”
kai Mairo ta girgiza “a'a nidai Gwaggo wanke min kafafu kawai take in zan kwanta bata min wanka”
“to mu wanka muke in zamu kwanta tashi ki cire kayanki”
tashi Mairo tayi ta nufi gurin da Momi ta nuna mata.
itama Momi tashi tayi ta shiga cire kayanta

saida ta gama wanka sannan ta kira Mairo tayi mata
tare suka fito  Mairo bata tsaya jiran komai ba ta faɗa saman bed
Momi kuma ta nufi waduraf tasa kayan bachi ta ɗaura zane sama bayan tasa hijab ta kabbarta sallah.

koda Momi ta gama sallah Mairo tayi bachi.
tana cire hijab ɗinta ta nufi down stairs.
bata daɗe ba ta shigo ɗakin da plate din abinci a hankali ta shiga tada Mairo amman hakan bai hanata farkawa a firgice ba.
“k'arɓi ga abinci kici saiki kwanta”
kin k'arɓa tayi ta tsurawa Momi ido can kuma ta mayarda su gurin abinci.

sakwarace da miyar agutsi da namomi hannun tasa ta k'arɓa “ni bazan iya cinyewa duka ba”
“ci kibar saura”
kusa da ita Momi ta zauna tana amsa waya.

saukowa Mairo tayi kasa ta hau cin abinci
cikin yan mintuna ta kare ta tashi tana suɗar miyar dake plate ɗin duk ta ɓata gurin da miya kamar mai ɓararen baki.
nunawa Momi hannunta tayi “na kare ina zan wanke hannuna?”
toilet Momi ta nuna mata
tana gyaran ɗaurin tawul ta shiga toilet ɗin

koda ta fito Momi ta gyara gurin tana mopping
tsaye tayi har momi ta kare ta nuna mata gado “hau ki kwanta”
ba musu ta hau Momi taja zanen rufa ta lulluɓa mata.
ta kashe wutar ɗakin ta kunna ta bedside lamp ta nufi kofa,
Mairo na ganin zata fita ta tashi da sauri “ni kaɗai zaki bari nan?”
Momi daga gurin da take tsaye tace “tsoro kike jine?”
“eh bazan iya kwana ni kaɗai ba”
“babu abunda zai sameki ki kwantar warki kiji?”
“aa ni bazan yarda ba”
saukowa tayi ta nufo Momi.
Momi tace “to bari na kunna miki wutar saiki kwanta kamin nazo yanzu zan dawo jeki kwanta”
lake kafaɗa tayi “a a ni bazan yarda ba”
tsawa momi ta katsa mata “wuce kije ki wanta nace”
jiki na ràwa Mairo ta faɗa saman gado ta ɗanne fuskarta cikin katifa,
Momi na ganin haka ta taja kofa ta fice

kuka Mairo tayi tayi kaɗankaɗan kuma ta kasa ɗago kan dan tsoron kar taga wani abu har bachi ya ɗauketa.

*_washe gari....._*
tunda asuba Momi ta tada Mairo
a firgice ta farka jikinta sai rawa yake hannun momi ta rika suka shiga banɗaki tare sukayi alwala.
bayan sun fito Mairo ta nufi yar zakarta ta zazzage ta ɗauki wata atamfar kauye tasa tare da hijab ta fara sallah,

tana sallamewa komai bata tsaya yiba  ta koma bachi.
sai 8 da minta ta farka koshi dan siraj ya tada tane.
da murje murjen ido ta tashi tana mik'a idonta a lumshe tana soma kiran gwaggo.
“ke tashi momi na kiranki nace”
‘to’ tace tana turo baki kamar ta fasa kuka
shidai bai tsaya jiranta ba ya fice,

saida ta gama gunguninta sannan ta tashi ta nufi kowa duk jin take bata son gidan,
tana fitowa ta hango farlo down stairs.
wani irin ihu ta saki saboda juwa data gani tayi bayabaya tana kiran “na shiga uku wayyo Gwaggo na bani mutuwa zanyi”

duk kai suka ɗago sun Kallonta daga dining area siraj ne ya fara tambaya “lafiya?”
cikin kuka tace “na bani bazan iya saukowa ba na shiga uku Gwaggo”
duk fashewa sukayi da dariya banda siraj da yaja tsaki sai kuma Momi data hau mata faɗa “ke wai wane irin iskancine dake haka haka kawai zaki rika yiwa mutane uhu”
Qasin dake tsaye ya kalli Momi yana murmushi “tsorone taji momi kinsan yar kauye ce”
“to dan taji tsoro sai tayiwa mutane ihu iskancin da takeyi can kauye nan bazan ɗauke shiba”
tea cup ɗin dake hannunshi ya aje ya nufi up stairs.

hannunta ya riko ta rumgumeshi iya karfinta ta kulle ido gam sannan suka sauko.
har suka isa dining bata buɗe idon ba saida taji an zauner da ita sannan ta buɗe ido tana kare musu kallo,

da Qasin ta fara sannan Usman, Siraj sai kuma ta juyo gun Nura.
kofin tea Momi ta aje mata idonta cike da hawaye ta ɗauka ta kai baki
bata ajeba saida tasha rabin kofin Siraj da Nura da Usman sai dariyarta suke Qasin Murmushi yayi ya kalli agogon hannunsa yace “Momi ni bari na wuce gurin aiki”
“to Allah ya tsare”
“Amin”
saida ya kara kurɓa tea ɗin sannan ya fice.

Usman ya kalli Mairo yana driya yace “bakison bredin hala?”
banza ta masa har Momi ta kare cin abincinta da Usman suka tashi.
sannan ta ɗauki bredin tana hawaye ta rika somawa kamar turo da miya tana ci.

© *Khadeeja Candy*

Post a Comment (0)