WASIƘA ZUWA GA ZUCIYA

💌 *Wasika daga Zuciya:*

✍ Mansur Sokoto
17 Ramadhan 1441H (10/05/2020)

*Abinda ke damu na:*
1. Duk inda na buga waya labarin mutuwa ake ba ni.
2. Idan na buda Facebook labaran mutuwa ne a ko ina.

*Fatawa:*
Kowa ka tambaya cewa yake yi: Ba Corona ce ba.

*Dalili:*
Masu mutuwar duk masu hawan jini ne da ciwon Sugar, sai kuma tsofaffi.

*Wata Tambaya*:
Tun yaushe ne suke dauke da wannan ciwon? Ko a satin nan ne tsufansu ya kama?

*Tambaya Ta 3:* 
A duk duniya ana ta mace-mace, kuma an yarda Corona ce musabbabi. Me ya sa tamu mutuwa ta bambanta?

*Abin lura:*
Idan mun yarda da matsala mun kama hanyar maganin ta. Idan ba mu yarda ba to, mun dauki matakin ci gabanta.

*Laifin wa ye?*
1. Wadanda ke da alhakin wayar da kan jama'a har yanzu akwai aiki babba a kan su.
2. Masu kutsawa a cikin abinda ba su sani ba suna daukar wa kansu nauyin da za su yi da-na-sani a kan sa.

*Babbar Matsala:*
Babu yarda a tsakaninmu da Jagororinmu na mulki da na addini.

*Addu'ata:*
Idan wannan ibtila'in shi ne ajalinmu, Allah ya karbi uzurinmu ya sa mutuwar shahada ce a gare mu.

*_Wassalam_*

Post a Comment (0)