ADMINS KU JI TSORON ALLAH 4


*ADMINS KUJI TSORON ALLAH!!! 04*

*RADDI ZUWAGA DOCTOR YAZEED (08092526064)*

*DAKTA MAI GANIN TSIRAICIN MATA A SOCIAL MEDIA*
.
.
*DAGA ZAUREN*
.
*MAJALIS - SUNNAH*
.
.
مجلس السنة
📓📔
+2349032091131
+237665087032
.
.
Yau 18/ 11/ 1441 wanda yayi dai-dai da 09/ 07/ 2020.
=
=
_Godiya ta tabbata ga Allah, muna gode masa, muna neman taimakonsa, kuma muna neman tsarinsa daga sharrin kawunanmu da munanan ayyuakanmu. Hakika Wanda Allah ya shiryar Babu Mai 6atar dashi, Wanda ya 6atar Kuma Babu mai shiryar dashi. Kuma Ina Shaidawa babu abinda bautawa da Gaskiya sai Allah shi kadai, kuma ba shi da abokin tarayya. Kuma Ina Shaidawa Muhammad bawansa ne Kuma manzonsa ne._

_Bayan haka, jama'a idan kuna tare damu munyi bayani gameda wani admin da yake zanen nonuwan mata, kuma yake tambayarsu su dinga turamasa hotunan nonuwansu, wanda wannan shine kadan daga cikin sharrinsa, saboda haka yan uwana mata sai ku kiyaye. Yau kuma insha Allah zamuyi raddi zuwaga wani zindikin mutum mai suna *YAZEED*._

_Tho jama'a shi dai wannan mutumin yana amfani da sunan *DOCTOR* a wassap username dinsa, amma na tabbatar ba doctor bane, sai dai shi doctor ne wanda yake kallon tsiraicin mata a social media kuma shi zindiki ne, domin nayi magana dashi na fahimci bama shida ilimin rayuwa balle a zo kan ilimin zamani har ya zama doctor, saboda haka asalin sunansa shine *YAZEED*, sannan yana zaune a tarauni a yadda na samu information._

_Jama'a wallahi wannan bawan Allah yayi nisa sossai wajan lalata iyayenmu da 'ya'yanmu da kannanmu. Sai da nayi kwana uku acikin group dinsa mai suna *Rayuwar jima'i* ina feel research akan abubuwan da ake aciki, jama'a abin bakin ciki da takaici shine yawancin mutanen ciki wallahi matan aure ne, saboda har hotunansu suke turowa acikin group kuma wallahi iyaye ne su manya, domin har da masu shekaru 50 da wani abu acikin group dinsa._

_Tho da na shiga cikin group din, banyi magana ba a ciki domin nasan idan nace zanyi musu naseeha a group, tho babu shakka zai cireni, saboda hakane yasa na dinga binsu daya bayan daya ina musu naseeha ina tsoratar dasu akan wannan group din har Allah yasa wasu suke ta fita daga cikin group din._

_Lokacin da na shiga group din na tarar da yan uwanmu mata kuma musulmai samada mutane dari biyu aciki, kuma wallahi duka mata ne kuma masu aure sunfi yawa acikinsu. Tho a jiya sai naga wata yar uwa tayi musu naseeha a cikin group din cewa wannan abinda suke wallahi ba dai-dai bane, sai wata tace ai Sunnah ce yin hakan domin koyon ilimin jima'i suke. Tho jama'a idan kun fahimci wannan da kyau zaku gane ashe jahilci ne yake damun matan mu suke shiga ire-iren wadannan groups din. Tho a haka dai cikin ikon Allah wasu suka fita ta sanadiyar wannan naseehar, nima sai na daura tawa naseehar acikin group din kai tsaye, sai Allah ya taimake mu mutane dayawa suka fita daga cikin group din ta sanadiyar naseehar da mukayi musu, duk da cewar akwai wadanda basu fita ba, yanzu haka mutanen da suke cikin group din yanzu basu wuce 80 ba, kuma insha Allah duk sauran suma sai sun fita._ 

_Tho jama'a muna cikin cigaba da wannan naseehar kwatsam sai mukaga Doctor ya ciremu daga cikin group din, tho ashe yar uwan tawa ta riga tayi masa naseeha ta private, kunsan me yace mata jama'a? Sai yace mata *"Ta bar naseehar ta, ba sai ya ji ba, wanda ya kwance masa zani a kasuwa baya zuwa yace zai dora masa a gida".* Jama'a ina ma'anar kwance masa zani a kasuwa? Shine tayi musu naseeha acikin group, dan haka meye na biyoshi private tayi masa naseeha kuma, bayan ta tona asirinsa a group. Wannan shine abinda yake nufi a takaice. Tho tambaya anan shine a gidan uwar wa irin wannan zindinkin ya Doctor? Tho amma na yarda shi doctor ne amma na kallon tsiraicin mata._

_Jama'a daga cikin sharri da iskancin mutumin nan mai suna *YAZEED* mazaunin tarauni wanda yake amfani da sunan *DOCTOR* a group dinsa shine, yace wai shi sunansa doctor me warware matsalolin ma'aurata. Kuji fah, jahili ne amma cewa yayi me warware matsalolin ma'aurata, wanda ko haukansa bai iya warwarewa ba, amma shi zai warware na mutane. A gidan uwar wa Yazeed zaka iya warware mana matsaloli??_

_Yadda yake warware matsalolin kuwa shine, zai bi matan mutane a private yace su turamasa hotunansu wanda sukayi a tsirara, tho masu hankali acikinsu sun gane cewa mutumin banza ne, don haka sai suka zageshi suka fita daga group dinshi, tho marasa hankali da tunani da ilimi acikin su kuwa sai suka tura masa, tho idan ya kalla yaji dadi sai yace ya gano matsalar su saboda haka sai ya tambayesu, su fadi matsokalar sha'awarsu (wato inda da an taba a jikinta take rikicewa). Jama'a wannan bai isa mata su gane cewa dan iska ne jahili ne shi? Jama'a kuji irin wadannan maganganun fah, tsakani da Allah ko baki shiga makaranta ba, ai yakamata kigane cewa mutumin banza ne shi, tho amma duk da haka wasu basu gane ba._

_Tho idan mace ta gane cewa zindiki ne jahili ne tho sai ta fita. Kuma idan suka fita still bazai hakura ba, sai ya bita private yace mata wallahi ke kwaila ce (wato zai fadawa wacce ta fita din ita kwaila ce) idan kuma tace ita ba yar kwaila bace ba, tho sai shi yace ta dauki boobs dinta ta turamishi don ya bata shawara. Tho haka dai mutumin nan yake lalata 'ya'yanmu mata da iyayenmu mata, kuma wani lokacin sai yace yanaso kowa tayi masa video din jikinta tsirara a turamasa, na rantse da Allah haka wasu suke ta turamasa, kuma wallahi da aurensu. Daga cikin wadanda suka tura masa videon jikinsu, tho sai wata ta gane cewa tayi kuskure saboda haka sai ta fita daga cikin group din, tho da doctor yaga ta fita, sai ya biyota private yace idan ta kuskura ta kara fita wallahi sai ya yada videon da ta tura masa a social media. Wallahi haka wannan matar ta zauna acikin group dinsa tana ji tana gani amma bazata iya fita ba. Saboda idan ta fita zai watsa hotunanta da videonta a social media kowa ya gani._

_Misalin wannan abinda ya faru da ita, tho irinta ne sak ya faru da wata yar film kwankin baya kadan mai suna *MARYAM BOOTH*. Jama'a kuyi hakuri saboda duk wanda sunansa ya kama tho zamu ambaceshi, haka duk wacce sunanta ta kama, tho zamu ambaceta, kuma idan akwai wani mai ja akan maganata, tho Allah ya tsine masa/mata idan bai fito ya wankesu duka daga nawa maganar ba._ 

_Ita wannan yarinya mai suna *MARYAM BOOTH* an dauketa video ne yayin da ta fito daga wanka kamar yadda ta fada, amma sai tace wani mawaki mai suna *DEEZEL* shine ya dauketa yayin da ta fito daga wanka, shi kuma mawakin sai ya turawa wani, shi kuma wanda aka turawa sai yayi ta mata barazana cewa zai fitar da videon idan kuwa ba haka ba, tho sai ta biya, haka dai suke mata barazana, kuma itama tana biyansu kamar yadda ta fada. Tho a karshe dai sai da suka fitar da videon, amma saboda rashin kunya irin na yan film, da rashin tarbiya irin na *MARYAM BOOTH* sai tace akwai Allah kuma Allah zai sakamata, haka tayi wannan maganar a shafinta na Twitter. Tho tambayarmu anan shine a gidan uwar wa za a saka miki? Shin meye kaiki hotel har kikayi wanka kika fito tsirara a gaban wani kato ya daukeki video? Amma kunji ta saboda rashin hankali irin na *MARYAM BOOTH* sai ta fito wai zata kare kanta. A gidan uwar zaki iya kare kanki? Sai dai ki kare kanki a gun marasa hankali, amma ba irin masu hankali ba. Tho jama'a idan kun fahimci wannan da kyau, zakugane maganar da nayi jiya cewa yan film suna bada gudummawa sossai da sossai wajan lalata mana tarbiyar 'ya'yanmu mata. Saboda irin wadannan yan iska yan film suke kallo suke daukar course aciki. Tho muna addu'a Allah Ubangiji yayi mana maganinsu, kuma Allah ya isar mana._

_Sannan daga cikin sharrin mutumin nan mai suna *YAZEED* mai amfani da sunan *DOCTOR* a WhatsApp dinsa. Kullum da safe sai ya turo da video clip na iskanci wanda ake cema XXX, tho idan ya turoda videon a karkashin videon sai ya rubuta kamar haka:- *Masu aure a gwadawa oga wannan da safen nan, bance marasa aure su bude ba, haka zalika bance wacce bataso ta bude ba, domin bana san cece ku ce.*, tho haka yake rubutawa duk safiya. Jama'a kunsan abun mamaki? Na rantse da Allah matan da suke cikin group din murna suke suna cewa, *Allah yasakada alkhairi, Allah ya biya, weldone, doctor aikin ka na kyau, you are the best, a karo wasu, doctor Dan Allah a karo wadanda sukafi zafi sossai,* da dai sauran ire-iren wadannan comments din, banga wacce ta fito tayi comment da rashin jindadin wannan videon ba._ 

_Tho idan kuka gane wannan da kyau, tho zaku fahimci cewa mutumin nan ba karamin lalata matanmu yake ba, saboda hakane yasa na saka lambarsa a sama, domin kuyi blocking dinsa, kuma ku sashi a blacklist, saboda nan gaba._ 

_Wannan aikin kuma duk safiyar duniya sai ya tura video da safe, yau din nan ma sai da aka turo, tho amma daya daga cikin yan group din ce ta turo, saboda itama ta kware. Tho jama'a tsakani da Allah idan watarana aka samu akasi aka cireta daga cikin group, kuna ganin itama bazata bude nata na iskancin ba ta koyawa wasu?? Saboda haka muna addu'a idan yanada rabon shirya, tho ya Allah ka shiryeshi. Idan kuma bashida rabo, tho ya Allah kayi mana maganinsa da ire-irensu, ka tsinemasa albarka, ka tozarta shi ka wulakanta shi, sannan ya Allah isar mana._

_Sannan duk wata mace da tasan tana cikin group din da bai dace ba, tho taji tsoron Allah ta fita ta tuba, idan ba haka ba, tho wallahi idan ta kuskura ta mutu da wannan groups din a wayarta, tho na rantse da Allah sai taci ubanta sai tayi nadamar da bazatayi amfani ba. Saboda haka dan girman Allah kuji tsoron Allah ku fita daga cikin groups din da basuda amfani, idan kuwa kikayi girman kai, tho zaki tarar da girman azaba, wato azaba mai girma. Sannan akwai wata mai sunan *MAMAN UNAIS* wacce itace mai yi masa tallar group dinsa, tho itama nan gaba zamu zo kanta insha Allah. Sannan duk wacce take da labari akan groups din da basu dace ba, tho tayi min magana, don mu ceci yan uwanmu mata, kuma itama zata samu lada insha Allah. Zan dakata anan sai kuma mu hadu a lekca ta gaba insha Allah, domin mu samu mu rage wannan 6arnar da yayi yawa a social media yanzu._
=
=
_Dan uwanku a musulunci_
°
*_✍Abdulrasheed Ibn Musa Abms_*
°
°
.
Allah ta'ala yasa mudace
.
.
https://www.facebook.com/Zauren-Majalis-Sunnah-420869088334488/?referrer=whatsapp
.
ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ.
Post a Comment (0)