*MAKARANTAR AZUMI 015*//
π ```KWAΖAITARWA WAJEN YIN SALLAR DARE```
Manzon Allah Ya kasance Yana ΖwaΙaitar da Sahabban Sa gameda yin tsayuwar Ramadana, kuma ya kwaΙaitar da Al’umma gaba-Ιayan ta akan haka, saboda faΙar Sa a Hadisin Abu Hurairah (RA) yace: Manzon Allah ο·Ί Ya ce: “ *Duk wanda yayi tsayuwar Ramadana yana mai Imani kuma yana mai neman Lada a wajen Allah, an gafarta masa abinda ya gabata na Zunuban sa* ”. [Bukhaariy da Muslim suka riwaito shi].
Don haka ya kamata ga mai Azumi yayi kwaΙayin yin Sallar Dare, kada ya bari wannan alkhairi ya kuΙuce masa, musamman a cikin wannan Watan akwai Daren Lailatul Kadri, kuma yafi watanni dubu alkhairi.
Kuma ita wannan Sallah, raka’o’in ta basa wuce raka’o’i goma sha-Ιaya, Annabi baya Ζarawa akan haka; saboda abunda Ummuna Aishah ta faΙa (RA) tace: *Manzon Allah (SAW) Ya kasance baya Ζara sama da Raka’a goma sha-Ιaya a Ramadan ko ba a Ramadana ba* . [Bukhaariy da Muslim suka riwaito shi].
Duk da yake ya halasta Mutum yayi Ζasa da hakan saboda aikin Manzon Allah (SAW) da ya aikata hakan, a yayin da yace: “ *Sallar Wutiri dai haΖΖi ce akan kowani Musulmi, duk wanda yake so yayi Wutiri da Raka’o’i biyar yana iya aikata hakan, kuma duk wanda yake so yayi Wutiri da Raka’o’i Uku yana iya aikata hakan, hakama wanda yake so yayi Wutiri da Raka’a daya ma yana iya aikata hakan* ” [Abu Dawuda ne ya ruwaito shi daga Sahabi Abu Ayyub].
✍ *ANNASIHA TV*
