KWAƊAITARWA WAJEN YIN SALLAR DARE



*MAKARANTAR AZUMI 015*//

πŸ“Œ ```KWAƊAITARWA WAJEN YIN SALLAR DARE``` 

Manzon Allah Ya kasance Yana Ζ™waΙ—aitar da Sahabban Sa gameda yin tsayuwar Ramadana, kuma ya kwaΙ—aitar da Al’umma gaba-Ι—ayan ta akan haka, saboda faΙ—ar Sa a Hadisin Abu Hurairah (RA) yace: Manzon Allah ο·Ί Ya ce: “ *Duk wanda yayi tsayuwar Ramadana yana mai Imani kuma yana mai neman Lada a wajen Allah, an gafarta masa abinda ya gabata na Zunuban sa* ”. [Bukhaariy da Muslim suka riwaito shi].

Don haka ya kamata ga mai Azumi yayi kwaΙ—ayin yin Sallar Dare, kada ya bari wannan alkhairi ya kuΙ“uce masa, musamman a cikin wannan Watan akwai Daren Lailatul Kadri, kuma yafi watanni dubu alkhairi.

Kuma ita wannan Sallah, raka’o’in ta basa wuce raka’o’i goma sha-Ι—aya, Annabi baya Ζ™arawa akan haka; saboda abunda Ummuna Aishah ta faΙ—a (RA) tace: *Manzon Allah (SAW) Ya kasance baya Ζ™ara sama da Raka’a goma sha-Ι—aya a Ramadan ko ba a Ramadana ba* . [Bukhaariy da Muslim suka riwaito shi].

Duk da yake ya halasta Mutum yayi Ζ™asa da hakan saboda aikin Manzon Allah (SAW) da ya aikata hakan, a yayin da yace: “ *Sallar Wutiri dai haΖ™Ζ™i ce akan kowani Musulmi, duk wanda yake so yayi Wutiri da Raka’o’i biyar yana iya aikata hakan, kuma duk wanda yake so yayi Wutiri da Raka’o’i Uku yana iya aikata hakan, hakama wanda yake so yayi Wutiri da Raka’a daya ma yana iya aikata hakan* ”   [Abu Dawuda ne ya ruwaito shi daga Sahabi Abu Ayyub].

✍ *ANNASIHA TV*
Post a Comment (0)