RASHIN BIYAYYA DA KYAUTATAWA MAHAIFA YANA CIKIN MAFI GIRMAN ZUNUBI



RASHIN BIYAYYA DA KYAUTATAWA MAHAIFA YANA CIKIN MAFI GIRMAN ZUNUBI

Hakika Annabi ﷺ ya yi mana umarni kamar yadda Allah da kansa yayi mana umarnin akan yin biyayya da kuma kyautata mahaifa,da kuma hani daga sabawa masu da kuma cutar dasu,sabawa mahaifa da rashin kyautata masu yana cikin mafi girma zunubai da akewa yiwa Allah anan duniya.Annabi ﷺ ya baiyana mana illa da girman laifin mai sabawa Mahaifansa, ga kadan daga cikin su:-

*1-"Mai Cutar da mahaifansa Tsinanne ne inji Manzon Allah ﷺ *.

Daga Abu Hurairaita R.A yana cewa :-
"Annabi ﷺ yana cewa:-
*(La'antacce ne mai cutar da mahaifansa ko mai sabawa mahaifansa)*.
@ﺍﻟﻄﺒﺮﺍﻧﻲ ﻓﻲ " ﺍﻷﻭﺳﻂ
" ‏( 8497 ‏)
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ ‏( 2420 )

*2-"Allah bawa kallon mai sabawa Mahaifansa a ranar alqiyama*.
Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-
"Manzon Allah ﷺ yace:
*(Mutane guda ukku Allah bazai kallesu ba a ranar alqiyama:-
-Mai sabawa mahaifansa
-Wanda baya kishin iyalinsa...............)*
@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ "

*3-"Mai sabwa mahaifa baya shiga aljanna"*.
Daga Ibn Umar R.A yana cewa:-
"Manzon Allah ﷺ yace:
*(..............Mutane guda ukku bazasu shiga aljanna ba a gobe alqiyama:-
-Mai sabawa mahaifa
-Mai kwankwadar giya
-Mai yin gorin abinda ya bada)*
@ﻭﺭﻭﻯ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ ‏( 2562 ‏)
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﻨﺴﺎﺋﻲ "

*4-"babu mai shiga aljanna sai ya kasance yana biyayya ga mahaifansa kuma baya saba masu"*.
Wani mutum yazo wajan Annabi s.a.w sai yace Ya Manzon Allah ﷺ
"Na shaida babu abin bautawa bisa hakki da gaskiya sai Allah kuma kai Manzon Allah ne, kuma nayi salloli biyar na farilla kuma na bada zakka kuma nayi azumin watan Ramada?? Sai Annabi ﷺ ya ce:
*(Wanda ya mutu akan haka yana tare da Annabawa da Shahidai Siddiqai a ranar alqiyama matuqar bai sabawa Mahaifansa ba)*.
@ﻭﺭﻭﻯ ﺃﺣﻤﺪ ‏( 24299 ‏)
@ﻭﺻﺤﺤﻪ ﺍﻷﻟﺒﺎﻧﻲ ﻓﻲ " ﺻﺤﻴﺢ ﺍﻟﺘﺮﻏﻴﺐ " ‏( 2515 ).

*5-"Allah baya karbar aiyuka na mai sabawa mahaifansa inji Manzon Allah ﷺ "*
Daga Abi Umamah R.A yana cewa:
Manzon Allah ﷺ yace:
*(Mutanan guda ukku Allah baya karbar aiyukan su na farilla da na nafila:-
-Mai sabawa Mahaifansa
-Mai gorin abinda ya bayar
-Wanda yake karyata Qaddara)*.
@ﺭﻭﺍﻩ ﺍﺑﻦ ﺃﺑﻲ ﻋﺎﺻﻢ ﻓﻲ "ﺍﻟﺴﻨﺔ " ‏( 323 ‏)
@ﺳﻠﺴﻠﺔ ﺍﻷﺣﺎﺩﻳﺚ ﺍﻟﺼﺤﻴﺤﺔ " ‏( 1785 )

*6-"Sabawa mahaifa yana cikin mafi giraman zunubai inji Annabi s.a.w*.

Manzon Allah ﷺ yana cewa:-
*(Shin bazan fada maku ba mafi girman zunubi ba??)*sai Sukace:Eh ya Manzon Allah ﷺ ,sai yace;
*(Yin shirka da Allah da Kuma sabama Mahaifa)*ya kasance yana Kishingide sai ya tashi zaune sannan yace;
*(Ku saurara da maganar zur da Shaidad Zur)*
@ﻣﺘﻔﻖ ﻋﻠﻰ صحته.
Allah ka nisantar da mu daga aikata abinda zai sanya mu sabawa Mahaifanmu.Allah ka jikansu kamar yadda suka kulamu lokacin muna yara.

*Allah ka gafarta ma mahaifan mu baki daya*

SUBSCRIBE TELEGRAM CHANNEL:👇
https://t.me/DailyHadithss
Post a Comment (0)