ZUNUBAI GUDA BAKWAI 7️⃣ MASU HALLAKARWA

ZUNUBAI GUDA BAKWAI 7️⃣ MASU HALLAKARWA


 :
*TAMBAYA*❓
:
Assalamu alaikum Mal. wadanne abubuwa ne guda 6 da Annabi yace mu gujesu suna hallakar da dan adam
:
*AMSA*👇
:
 Wa'alaykumussalam, To dan'uwa abubuwan guda bakwai ne kamar yadda suka zo a hadisin Bukhari mai lamba: 6857 da kuma Muslim a lamba ta: 262, inda annabi ﷺ yake cewa: ku guji abubuwa guda bakwai masu hallakarwa: 
1. Shirka da Allah. 
2. Sihiri 
3. katshe rai ba tare da hakki ba 
4. Riba. 
5. Cin dukiyar maraya. 
6. Juya baya a wajan yaki. 
7. Yiwa mata katangaggu kazafi. 

Allah ne mafi sani. 

 Amsawa:-Dr. Jamilu Zarewa.

Ku kasance damu domin ilimintarwa, Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
KU BIYOMU A TELEGRAM:👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
KU BIYOMU A FACEBOOK👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177

Ku taya mu isar da wannan sakon ta hanyar SHARING wasu da yawa zasu amfana. 
Post a Comment (0)