UKU-BALA'I 08

UKU-BALA'I

NA

KAMALA MINNA.
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*


​​WÉ› ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucÉ‘tÉ›, MѳtiѵɑtÉ› ɑɳɗ ɛɳtɛʀtÉ‘iɳ ѳuÊ€ ʀɛɑɗɛʀร​.


BABI NA TAKWAS.

Sun jima cikin shiru aka rasa mai tankawa a cikinsu, domin sun saki baki ne suna jiran cewar Likita. kamar yarda shima yayi shiru, yana nazarin ta inda zai fara yi musu bayanin lamarin.
Ihun da ya karaÉ—e dakin ne ya dawo da su daga duniyar shiru da na tunanunnuka da suka faÉ—a a firgice duk sukayi kanta cikin matsanancin tashin hankali sosai take ihu gami da fizge fizge tana hada kanta da karfen gadon da take hannayenta duk biyu ta rufe kunnuwanta da su da sauri Mariya ta isa gareta tana kokarin rike amma wani wawan fizga da tai gabadaya Mariya tayi kasa ta zube hakan da Bello ya gani da sauri ya isa gareta da taimakon likita shiga kokarin riketa amma ina! wani karfi ne ya ke zuwa mata lokaci guda sosai take fizge fizge su kan su sun rasa yarda za suyi su riketa sai da sukayi da gaske sannan Bello ya samu da kyar ya rike hannayenta ya hadata da jiminsa ta kankame amma gabadayam su sai jikinsu ya kara shiga wani irin shock kamar an jona su da wayar wutar nepa sai mazari jikinsu ke yi.
Da ƙyar da soɗin goshi suka samu fizge fizgen nata ya ragu dalilin irin rikon da Bello yayi mata ba na wasa bane.
Kuka ne ya sake karaÉ—e dakin amma wannan karo kukan yao ne dake cam yashe wanda sam suka manta da lamarin sa tun da suka shigo Asibitin.
Gabadaya sun manta dashi, sun manta sun zo da wani dangin rai bayan su gabadaya suka juya suna kallon daga in da kukan yake tasowa suka shiga kallon-kallo a tsakaninsu.
Mariya ce ta mike da gudu cikin tsananin faduwar gaba ta isa gareshi ta sungomo shi gami da haÉ—eshi da jikinta wani irin tausayin sa da kauna taji yana kara wanzuwa cikin jikinta sosai take jin tausayin sa hawaye sai zuba suke saman fuskarta suka gangarowa bayansa gyaÉ—a kai kawai take yi komai gani take yi yana faruwa kawai amma ta rasa komai na hayyacinta komai kara rikice mata yake yi.
"Yaa Rabbi!".
ta fadi cikin tashin hankali kafin ta fara tafiya cikin É“arin jiki ta isa ga Doctor dake ta faman kokarin ganin Habeeba ta daina fizge-fizgen da take yi.
"Likita Taimako don Allah kar bugun yayi yawa na tabbata in dukan yayi yawa komai zai kara jagulewa kanina don Allah ina bukatar rayuwarsa shima shi kadaine dan'uwa na a duniyar nan uwa daya uba daya...".
ta tsahirta da maganar da take yi kirjinta taji yayi mata nauyi sosai da sosai kafin ta sake kokarta daga laɓɓanta.
"Tun da ya zo duniyar nan..ya fara cikin karo da komai da komai na rashin jin dadi ko..ko abinci bai iya samun ci ba a duniyar nan".
yanayin sautin da ta ajje furucinta dauke da kuka yayi matukar shigar da likita cikin wani irin yanayi da sauri Dr, Aqeel ya dago kan sa dake wajan Habeeba wacce izuwa wannan lokacin fizgar da take yi ya lafa illa numfashi mai karfi da take ta faman ajjewa.
Sosai yake kallon Mariya yana jin tausayinta na shiga ko wani lungu da saƙo na jinka sa numfashi ya ajje ya na duban Bello a hankali ya furta.
"Gaskiya ne wai haka ba ku ba shi komai ba?".
Gyada kai ya shiga yi domin bai san abin da zai ce da Dr.Aqeel ba. bashi da abin cewa komai ya sauya masa tunani hankalinsa na kan Habeeba ya sani yana son É—ansa amma kuma ita rayuwarta ya fi so sosai da sosai.
"Uhmm amma likita...".
Ido ya zaro waje sosai yana duban Bello cike da fargabar abin da yake sanar dashi wanda lokaci guda ya gasgata maganar Mariya.
"Eh haka ne kenan?".
Dr.Aqeel ya tambaya idanuwansa kafe akan Bello. kai ya shiga gyaÉ—a masa alamar haka sosai da sosai Dr.Aqeel abin ya taba masa zuciya tausayin jaririn yana É—alsar masa a rai da ko ina na jikinsa da sauri ya waiga ya kalle shi hannun Mariya yanayin yarda yaga yasaka hannayensa a baki ya tabbatar masa da haka din.
Da hanzari ya fice daga dakin ransa a bace cikin yanayin ganin rashin kulawarsu da nuna adalci ga É—ansu da suka haifa bai kamata ace É—a jariri dan kwana daya ba ya fado duniya ya ci karo da horan yinwa ina wannan ba adalci ba ne sam!.
"likita ana bashi ruwa fa".
Bello ya fadi cikin É—arÉ—ar ganin yanayin da Dr.Aqeel ya nuna a fuskarsa hakan ya tabbatar masa ba su kyauta ba sam!.
sarai! Dr.Aqeel ya ji abin da Bello ya fadi amma hakan bai rage masa jin haushin da yake yi akansa ba.
Mintina goma ya shafe sannan ya koma cikin dakin hannunsa dauke da flas na jariri wacce take dauke da tatacciyar madara wacce ta samu hadi sosai sai gorar ruwa kuma shima dai da ka gani za ka gane na bukata jariri rai ne shigowarsa ya sanya Bello saurim miƙewa daga zaune da yake ya zabga tagumi hannu bibbiyu ita kuwa Mariya har wannan lokacin tana tsaye rungume da karirin.
ko Kallon in da Bello yake bai yi ba ya doshi Mariya.
"Zauna".
ya fadi yana mai janyo mata kujera dake girke kusa da ita ba musu ta zauna idanuwanta akansa ganin yanayin da fuskarsa ta nuna na rashin wasa.
Mika mata flas din yayi, ba musu ta sanya hannu ta amsa duk da dai ba ta san ya za tayi masa ba duk da dai ta fahimci abin da yake nufi da abin da ya bata sai dai ta ya ya za ta bude har tayi amfani dashi a dan tsora ce ta dube shi.
"Uhmm ya zan yi?".
bai tanka mata ba illa amsa da yayi ya buɗe mata gami da kaiwa bakin yaron sannan ya saki alamun ta riƙe da sauri ta rike ta sake gyara mata zama a bakin yaron kamar wanda yake ji a dora masa haba! ai sai ya shiga ja kamar zai tsinke bakin har wani sautin kara ke fita na tsotsa da yake yi dosai yake sha Mariya tana kafe da ido sai take jin tausayinsa ta na jin haushin rashin bashi abinci da ba su yi ba ta san laifin su ne a ciki sosai da sosai.
Wata irin ajiyar zuciya ta saki mai karfi ta daga kanta ta dubi Dr. Aqeel da ya kure yaron da kallo yana jin tausayin sa sosai.
"Godiya mai yawa likita".
Dubanta yayi kafin ya dauke kansa ya fara taku daya bayan daya har ya isa ga Habeeba a daidai lokacin wata Nurse ta shigo hannunta dauke da wani farantin silba mai kyau sai dauƙar ido yake yi ta iso gaban Dr.Aqeel ta tsaya gami da rinsinawa alamun girmamawa.
Hannu ya saka ya dauki abin gwaji da suke amfani dashi mai kama da iyafis sanyawa yayi a kunne sannan ya tunkari kirjin Habeeba da dayan bangaren abun a hannunsa ya dora sosai yayi shiru cikin natsuwa yana fahimta komai gami da gyada kai yana jujjuya idanuwansa tsayin wani lokaci kafin ya sauke ajiyar zuciya mai karfi ya zare abun idanuwansa akan Habeeba wacce itama idanuwanta a buɗe suke akansa a hankali ya dauko ledar ruwan (drap) dake kan faranti ya ratayeta akan dan dogon karfen dake girke a bakin gadon sannan ya dauko wata allura ya tsira cikin ruwan har guda biyu a hankali ya fara kokarin gyara mata hannu sosai yake kula da yanayinta bai som a samu wata mata yake yi a zuciyarsa a hankali ya tsira mata allura a jikin fatar hannunta yayi saitin komai yana kula da yanayin ruwan fara kokarin shiga jikinta sosai ya gyara mata komai kafin ya dube wanda ko gezau ba tayi ba da allurar ta shiga jikinta murmushi yayi wanda iyakarsa laɓɓan bakinsa.
Bello da tun ɗazu yayi ka sake yana kallon sarautar Allah sai yanzu ya ajje numfashi har da 'yar guntuwar kwallarsa duban Dr.Aqeel yake sosai yake jin kaunar sa a ransa yana jin yarda jindadin abin da yayi masa yake ratsa masa zuciya bai san da wani baki zai masa godiya ba bai san da wani ido zai kalle shi yace dashi ya gode ba ya san duk wata godiya da zai masa tayi ƙanƙanta zai yo masa fatan alheri dafatan nasara cikin rayuwar duniya da lahira.
shiru yayi sosai yana jin wani abu nayi masa yawo akai batun kudi dole ya nemo kudi domin yasan dole a bukaci kudi cikin lamarim nan gabansa ne ya yanke ya fadi lokaci guda ya shiga ambaton HASBULALLAHU WANI'IMAL WAKIL
sosai yake jin tashin hankalin abin da zai faru nan gaba kadan me zai ce da wannan likitan mai mutunci da YAƘANA me zai ce dashi in ya dauko masa batun neman kudi.
'Yaa Rabbi!'
ya ambata a zuciyarsa wani irin gumi ne yaji yana keto masa ta kowani kafar gashi dake jikinsa sosai yake jin gumin na gangara saman fatarsa sosai bugun zuciyarsa yake ji yana É—aduwa
"Raina ya baci matuka gaya akan abin da kuka aikata ga wannan rai da bai san komai ba a duniyar nan. Bai kamata ace daga fadowarsa ya fara gamu da BALA'I na horon yunwa bai ya kamata ace kun bashi kulawa a matsayinsa na wanda bai san kansa ba bai san wanene shi ba, bai san ya zai yi ya kula da kan sa ba, bai sam ya zai yi abu wani abu a rayuwarsa ba, sosai da sosai naji haushi".
Ya karashe yana lanƙwasa yan yatsun hannunsa suna fidd sauti juya yayi ya dubi Mariya da ta kafe shi da idanu hannunta rike da flas din da alamun jaririn ya sha yayi nakas har yaji ba wani sauran gurbi da yayi saura a cikinsa da sauri ta sauke kai ganin yana kallonta.
"me yasa kika daina bashi?".
ya fadi yana mai da kallonsa ga yaron da yayi shiru yana lumshe ido kamar mai son bingirewa da bacci.
Kanta akasa ta fara motsa laɓɓanta.
"ya koshi ne na gani, ina sanya masa ya na turewa".
GyaÉ—a kai kawai yayi ya dubi Habeeba wacce a wannan lokaci bacci mai nauyi yayi gaba da ita. ajje numfashi yayi mai dan karfi.
"wani hali muke ciki likita?".
Bello ya kokarta fadi cikin rashin abin fadi, yanayin da yayi maganar gabansa na bugu kadan kadan domin bai san amsar da za a bashi ba.
"sosai take cikin damuwa sosai rayuwarta ke cikin matsala sosai komai na rashin jindadi yake yawo a duniyar rayuwarta na san ka san haka".
Dr.Aqeel ya fadi yana mai kafeshi da ido kallo ne yake yi masa na TUHUMA da son karin bayani da kuma son samun wasu abubuwa masu kama da satar amsa akan lamarin.
Shiru yayi abubuwa da yawa suke dawo masa akai game da Habeeɓa da irin halin da yasan tana ciki na rashin jindadin rayuwa da damuwa kuma dake ci mata dunduniyar duniyarta gyada kai yayi gami da duban Habeeba sosai yake jin tausayin ta a ransa da ma jiki baki daya.
"Haka ne".
ya fadi cikin raunin Murya.
"mai yasa haka, meye dalilin faruwar haka, kasan kuwa illar dake samu mace mai ciki in tana cikin damuwa kasan wahalar kuwa da take gamuwa da ita kasan irin kuncin rayuwar da take shi kuwa...".
Ya tsahirta da zancen nasa ya na faman ajje numfashi.
"ba kuyi mata adalci ba a rayuwa sam! ya kamata ace tana samun kulawa da kwanciyar hankali a gareku da kuke kusanci da ita sosai da sosai ba ma wannan ba yanzu kusan halin kuwa sa take ciki kusan abin da ke tafe da rayuwarta yanzu kuwa to a gaskiya komai zai iya faruwa da ita a kowani irin lokaci".
"kamar ya?".
Mariya ta furta ba tare da tashirya yin furucin ba zumbur ta mike tsaye idanuwa warwaje take duban Dr.Aqeel sosai take jin maganganunsa na saukar mata da tashin hankali mai matukar yawa zuciyarta ta shiga zarya kirjin ta na bugu sosai.
"Don Allah...".
"kiyi shiru tukunna".
Dr.Aqeel ya tare ta daga maganar da ta dauko tun kafin ta dire.
"ta gamu da cutar jinjiga wacce a turance ake kira da eclampsia a na samun tane dalilin yawan damuwa in har mai ciki tana da damuwa har tayi mata yawa ta kan haifar mata da cutar hawan jini daga wannan lokacin har zuwa lokacin da za ta haihu komai zai iya faruwa da ita har ya kasance bayan ta haihu ta gamu da cutar eclampsia wato ciwon jinjiga".
ya tsahirta yana kallon su kamar yarda suma sukayi kasaƙe suna sauraron sa ya nisa gami da dorawa.
"cutar ta kan kasance ga mai ita kamar ta hauka mutum mai cutar eclampsia ya kan kasance kamar mahaukaci komai yakan iya sauywa na rayuwarsa ya kan kasance mai fizge fizge ko kuma ya dinga zunduma ihu a ko wani lokaci a takaice dai duk macen da ta gamu da irin wannan cutar tan zama tamkar mahaukaciya".
Sosai sautin kukan Mariya ke tashi cikin dakin kuka take yi wanda bai da sauti sosai amma hakan bai hana ya gauraye dakin ba sosai take jin tausayin Ummanta da ita kanta da Mahaifinta tun da Dr.Aqeel ya fara jawabin sa take jin komai na tashin hankali na wanzuwa gareta da sauri ta isa gareshi ta durkushe har tana kokarin sakin jaririn dake hannunta.
"Don Allah karka ce Ummata ciwon hauka take yi don Allah likita na roke da ka taimaka kar Ummata da gamu da wannan BALA'In cikin duniyar rayuwarta komai zai iya faruwa da kta ba ita ka dai ba har da mu".
Sosai kuka ya kwace mata tashiga yin sa kamar ranta zai fita.
Ido kawai Dr.Aqeel ya zuba mata yana kallon halin da take ciki sosai da sosai yake jin tausayinta karamar yarinya kamar ta amma ta fara gamuwa da irin wannan laro tun kafin ta gama sanin ita wacece duban Bello yayi wanda shi gabadaya ya gama susucewa hannu bibbiyu ya sanya ya tallabe haɓarsa sosai yake jin komai na rashin dadi na wanzuwa a gareshi sosai yake jin HAWAYEN ZUCIYA na safa da marwa a gareshi domin duk jarumtakarsa na hana idaniyarsa ZUBAR HAWAYE bai hana zuciyarsa kokawa ba.
A tausashe Dr.Aqeel ya sake dubansu cikin son kwantar musu da hankali.
"Idan mace tana zuwa awon ciki akai akai likitoci kan yi saurin gano za ta iya kamuwa da eclampsia ta hauhawar jininta. Dan haka za su yi iya kokarinsu gurin ganin sun dakile aukuwar hakan, ta gurin ba ta shawarwari da kuma magunguna. Amma matan da basa zuwa awo sun fi kamuwa da cutar ta eclampsia mai kama da ciwon hauka. Duk da ce wa wasun ma ko suna zuwa asibitin suna kamuwa da ita.
Idan mace ta hadu da ciwon kwakwalwarta ce kan juye tamkar na mahaukaci. Dan za ta yi ta surutai da hauka ba tare da ta san tana yi ba. Amma idan aka dage da magani za ta warke.
Wasu kuma idan abin ya taba su sosai ko da sun warke rayuwarsu za ta canja ba kamar da ba, maganarsu da mu'amalarsu da kun gani za ku ce sun taba hauka".
dakyar! ya tsahirta ganin wani tashin hankali da ya sake wanzuwa a fuskokin su ba kamar Mariya domin kukanta kara tsananta yayi cikim haka ta shiga kanƙame yaron dake hannunta sosai hawaye ke zuba a fuskarta.
"Shikenan ta faru ta kare".
abin da ta iya fadi kenan cikim hanzari ta mike daga durkushen da take ta nufi in da Ummanta take kwance cikin halin barci sosai dubanta take yi sosai kafin taja wani Numfashi mai karfi tana kara kanƙame yaron dake hannunta ta daga laɓɓanta dakyar domin jin kirjinta take yayi mata nauyi sosai kamar an dauko katon dutse an dora mata.
"wai da gaske Ummata damuwa kika saka a ranki wai haka ne inji likita...".
ta tsaya da maganar tana cizon laɓɓan bakinta na kasa tana mai nuna Dr. Aqeel kafin ta dora da cewa.
"me yasa haka Umma mai yasa kika saka damuwa a ranki har hakan ta faru ina son ki sosai da sosai Ummata bana son abin da zai taba min rayuwarki don Allah ki tashi sannan ki ciwa likita kin cire damuwar da yace ki na saka wa a ran ki san hakan zai sanya wannan cutar da yace kina da ita zata bar ki bana son komai ya zamto da gaske bana so naji wannan DAYA BALA'I akan ki don Allah ki tashi ki fidda komai a rank...".
"Mariyaa".
Cak! ta tsaya da maganar ta ta jin muryar da ta ambaci sunanta cikin sauti mai dauke da kin abin da take fadi.
"Ya haka Mariya ƙaddara ce hakan jarabawa ce daga Rabbi!".
sosai ta juye ta na duban Dr.Aqeel sosai take jin sautin maganarsa na amsa kuwwa akanta sosai take jin za ta iya yin shiru ta amshi maganarsa amma ba tabbacin zuciyarta za ta iya amsa kau da kai tayi.
Bello ne ya taso cike da sanyin jiki ya isa in da Mariya take ya janyota jikinsa yana bubbuga bayanta yana jin yarda zuciyarta ke harbawa sosai cikin sakanni yama jin yarda tausayinta ke ratsa masa zuciya sosai yake jin zafi a ransa game da wannan lamari.
Sun jima cikin wannan hali tsayin lokaci ba wanda yayi kokarin yin magana a tsakani Dr.Aqeel yayi gyarar murya kafin yace,
"ya kamata ace izuwa wannan lokaci kun gayyato natsuwa cikin duniyarku...".
"Ya ya hakan zata kasance Likita".
Sai lokacin Bello ya samu motsa laɓɓansa ya furta hakan.
Sosai Dr.Aqeel yake dubansa musamman tashim hankalin da ya hango girke cikin idanuwansa ya sani dole su ji ba dadi dole si u ji wani iri a ransu musamman irin wannan lamarin da yake da wuyar gane akan wanda mai sansh ba ya sani dole su tsorata sosai da lamarin saboda ganin bakon abu ne a garesu.
Sai dai abin da Dr.Aqeel bai sani ba abin da ke damun Bello shi lamarin Habeeba ya yarda za a bukaci kudi da ya san ba shi da su sam! a bangaren halin da Habeeba ke ciki ya sani komai daga Allah ne komai in ya faru da bawa muƙaddari ne to ya dauka komai ya faru da Habeeba Ƙaddararsu ce daga Rabbi! ba yarda za suyi zai sanya hammu bibbiya ya karba.
"likita naji bayanin kumana gode, da wannan fahimtarwa da kayi akanmu mage da rashin lafiyar da Habeeba ke ciki sai dai kuma Uhmm...".
Sai kuma yayi shiru ganin irin kallon da Dr.Aqeel ke yi masa mai dauke da murmushin karfafa guiwa ya nisa.
"kar ka damu komai zai zo da sauki da yardar Allah".
Gyada kai kawai yayi ba tare da ya sake cewa komai ba Dr.Aqeel ya mike yana mai duban Mariya dake takure waje guda sai ajiyar zuciya take kamar wacce tayi gudun ceton rai.
"ki kula dashi sosai in ya tashi kafin na dawo ki sake bashi madararsa ga ruwa nan ma zaki iya bashi amma dai ya fi kyautatuwa ki bashi madarar kawai".
gyada kai kawai take yi domin bata da karfin iya bude baki ta ce wani abu don ji take bakin nata yayi mata nauyi sosai da sosai.
"Mun gode".
Bello ya fadi lokacin da Dr.Aqeel ya juyo da kallon sa gareshi ya fara tafiya domin barin dakin.
"zan dawo nan da minti talatin don Allah ku kula sosai komai kuka ya faru kuyi hanzarin nema na kafin lokacin dawowa ta".
Daga nan bai sake cewa komai ba ya fice daga cikin dakin yana duban hannunsa mai daure da wani ratsattsan Agogo mai kalar whiter and Blue sosai Agogon ya dace da hannunsa mai cike da kwantacciyar suma baka mai dan haske sannu a hankali yake takunsa cike da natsuwa har ya karasa ficewa daga cikin dakin idanuwan Mariya na kansa sosai take son halin mutumin mai tattako lokaci guda taji yna burgeta domin taimakon da yayi mata ba ita kadai ba hatta mahaifinta DR. AQEEL MUNKA'IL ya burgeshi sosai da sosai.
Post a Comment (0)