UKU-BALA'I 17

UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​WÉ› ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucÉ‘tÉ›, MѳtiѵɑtÉ› ɑɳɗ ɛɳtɛʀtÉ‘iɳ ѳuÊ€ ʀɛɑɗɛʀร​.
   *Ita gobarar zuciya ruwa ba zai kashe ba, so ne ginshikin halinta. ba kowa ke sani ba*
     --ISA AYAGI😘
BABI NA GOMA SHA BAKWAI.
Abu mai girma taji ya zo mata wuya ya tsaya cak! Numfashi ma da kyar ta ke jansa don ji take kamar zata shiÉ—e a hankali ta kai hannayenta duk biyun ta dafe kanta da take ji yana kokarin tawatsewa sosai take jin kirjinta na buga a duk sakan sai take hango tashin hankalin da ta gan shi a ciki sosai take hango yanayin fuskarsa mai dauke da kayan damuwa masu girma sosai.
Sosai take jin wani abu mai kalar tausayi yana saukar mata a wani sashi na zuciya yana haifar mata da wani yanayi mai sanya kasala da sanya wani wani ciwo mai girma.
Ba ta san ya zata yi ba, ba ta san me take ji game dashi ba, ba ta san mai zuciyarta ke kokarin yi gareta ba, ba ta san mai yasa tunanin wannan mutumin yake kokarin samun waje a filin zuciyarta ba, ba ta san mai yasa komai ke kokarin wargaje mata da tunaninsa sa ba ta tsane shi bana ta son ko ganin fuskarsa a filin rayuwar duniyarta sosai take jin É—aci da bauri a zuciyarta duk lokacin da ko sunansa taji sai taji kamar ta kurma ihu amma a halin yanzu wani irin yanayi take ji game dashi sosai KUDIRI da tayi akansa a zuciyarta taji yana kokarin rushewa sosai taji bangarori na sashin zuciyarta sun kasu kashi biyu suna faman tamka muhawara wanda hakan ba karamin sanya ta tashin hankali yayi ba wanda ita kanta ba ta san mai ya dace tayi ba, ba ta san mai ya dace tayi akan wannan lamarin na zuciya ba.
A hankali take sauke hannayenta daga kanta idanuwanta take rintsewa tana buÉ—ewa a hankali gani take yi komai da yake faruwa da ita a yau kamar mafarki ne ba gaskiya ba za ta so ace a cikin barci ne komai ke faru da ita za ta so ace ba a zahiri bane za ta so ace kamar tatsuniyar kanzon kurege ne wannan lamarin.
Sosai take jin wani sashi na filin zuciyarta na halittar wani abu mai girma wanda yake kara tsuke mata da zuciya a duk sakan sosai take jin jikinta na samun wasu abubuwa da su ka danganci zuciyarta sosai take jin duk wani sashi na jikin ta na amsar abin da zuciyarta ke halitta ba ta san a yarda zata dauki abun ba bata san a wani irin ma'aunin hankalin ta zata ajje wannan lamarin ba komai take ji sabo na halitar kansa da kansa a zuciyarta da gangar jikinta.
Nisawa take yi a hankali tana faman fizgar numfashi wanda take jinsa kamar yayi mara karanci sosai a gareta.
A hankali ta fara kokarin tashi saman kafafuwanta tana jin yarda suke wani irin kokarin kasa daukar gangar jikinta sosai take ji wani abu mai sanya rauni a duk sassar jiki da zuciya yana samun gurbin zama a jikin nata.
Safah da Marwa ta shiga yi cikin rashin tsammanin abin dake faruwa da ita ba ta san mai zata ce ba mata san wani irin tunani ya kamace ta ba bata san mai rayuwart take kokarin dauko mata ba ta jiho filin duniyarta bata san wani irin tashin hankali bane ƙaddara ke kokarin dauko mata a wannan lokaci zuciyarta! Sosai take ji kamar ba ta ta ba sosai take ji kamar wata zuciyar ce ta daban ta sauya a filin kirjinta.
Komai take jin sa ba dadi sosai take jin saman harshenta na haifar mata da wani É—andano mai bauri gareta sosai take jin zafin da zuciyarta da can kasar ruhinta suna kokari kwatar kansu a kansa.
A hankali ta fara taku har ta isa inda Mu'azzam ke kwance idanunusa biyu da alamun farkawa tayi daga barcin da yake yi sai faman wasa da hannayensa yake yi yana kaiwa bakinsa yana tsotsa alamun yinwa yake ji.
Sosai ta ware idanu akansa tana kallon sa mamaki ne sosai ya bayyana a gareta bata ji mptsinsa ba kuma da alamun ya jima da tashi daga barcin a hankali ta mika hannayenta ta dauko shi gami da rungumeshi sosai ajikin ta sosai take jin wani irin yanayi game dashi sosa take jin so irin na DANGANTAKAR YAN'UWANTAKA na ratsa ko ina najinta sosai take jin so dan'uwan nata a duk lokaci tausayin sa da jikan ke kara samun gurbi a filin zuciyarta na kara haifar mata da so mai tsanani game da shi idanuwata take saukewa akan nasa tana faman sakin wani murmushi wanda ita kanta ba ta san tayi shi ba shima Mu'azzam din murmushin yake saki don akwai shi da arhar dariya.
"Ehem! Nikam ina jiye miki ranar da za ta zo ta kasance ta rabuwa da Mu'azzam ban san ya zaki yi ba?".
Kamar daga sama ta tsinkayi muryar Dr.Aqeel na dukan kunnuwanta sosai taji wani irin faduwar gaba ta ziyarce ta a hankali taji takunsa na iso gareta sosai take ji a jikinta idanuwansa na kanta sosai take jin komai na jikinta ya zama kamar ba nata ba ita kam! ba ta san abin da ke dawainiya da ita ba a duk lokacin da Dr.Aqeel ya fado duniyar rayuwarta sosai take shiga wani yanayi na rashin gane kanta.
A hankali ya karo ya ja kujera ya zauna yana fuskantar ta sosai fuskarsa kunshe da murmushi
"Umma ba ta tashi bane har yanzu?".
Ya fadi yana kai dubansa ga tsintsiyar hannunsa mai dauke da wani hadadden Agogo Gold-Colour kirar Rolex sai faman sheki yake yi yana kara wa hannun nasa wani irin kyau na musamman.
"Uhmm ba ta tashi ba. amma... Ai kai kace sai nan da awa uku kuma naga daga lokacin da kayi mata allurar zuwa yanzu ba a ci awanni uku".
Yanayin yarda take ajje kalmomin da take kokarin furtawa da laɓɓanta a hankali hakan ya shagalar da shi sosai komai cikin natsuwa da hankali take yin sa kamar mai tsoron kuskuren fadin wata kalma daya da bata dace ba gyaɗa kai yayi gami ya sake kai dubansa ga Agogon hannunsa.
"Yaa Allah! Kin ga shaf! na mance Wallahi".
Ya fadi yana fama yatsine fuska gami da dafe kai.
Yanayin da yake nunawa sai ya sanya Mariya sakin baki tana kallonsa sosa take kallon yanayin da yake nunawa kamar karamin yaro sai faman turo baki gami yake yi yana cizon laɓɓansa.
Ta gefen idanu ya kalle ganin yarda ta saki baki tana kallonsa sai ya cigaba da abin da yake yi don ya lura abin da yake yi din ne ya shagalar da ita cikin kallonsa sam bata lura ba tsayin lokaci har Mu'azzam dake hannunta ya kusan zuwa kasa cikin hanzari Dr.Aqeel ya kai hannayensa duk biyun ya tallebe shi wanda ita ma a daidai lokacin ta zabura ta kai hannunta domin gyarashi aiko sai hannayensa suka sarkeda na juna wani irin Shock ne gabadaya ya kama jikinsu da sauri Mariya tayi baya gami da sakar masa da Mu'azzam din idanuwanta a warwaje sai faman yarfe hannayenta take yi fuskarta na ya mutsewa kamar zata yi kuka.
Yaa Salam!.
Abin da ya fadi kenan cikin zuciyarsa da wani irin yanayi wanda ya kasa gane na menene sosai ya rungumi Mu'azzam amma har zuwa lokacin jikinsa bai daina sanar dashi Shock din daya ji ba.
Bugun zuciyarta sosai ya kara sauri sosai take jin wani tashin hankali yana samun waje a jikinta da zuciyarta da can kasan ruhinta sosai take jin wannan yanayi mai ABOTA da bakon lamari wanda tun da take bata taba jin irinsa ba mutane da yawa suna sarkewa bisa rashin sani amma bata taba jin irin wannan yanayin ba.
Wani fili na zuciyarta ya shiga sanar da ita:-
'shin kin manta waye kuka yi haka dashi. shin kin manta É—a namiji ne kuma hakan sam bai dace ba mace da namiji su taba juna in har ba muharraman juna bane'
Astagafurullah wa'atubu ilai!
Abin da ta fadi kenan cikin zuciyarta wani irin tsoro taji ya game jikinta da sauri ta fara ware idanunta domin karantar yanayin sa bata fuskanci komai ba domin hankalinsa ma bai gareta yana can wajan Mu'azzam yana gyara masa kwanciya a jikinsa hakan da ta gani ya sanya ta samun natsuwa domin abin da zuciyarta ta fara hasaso masa ba hakan bane.
"Amma dai yanzu Mu'azzam ya tashi ko. Naga yanayin barci game dashi".
Kai ta shiga gyaÉ—a masa kamar yana kallonta domin ta kasa cewa komai bakin ta take jin yayi mata nauyi sosai tsoron magana take yi domin bata san mai zata ce ba jin jikinta take yi har yanzu shock din bai sake ta ba.
A hankali ya dago idanuwansa jin bata ansa masa ba sosai yake kallonta ya ganin yanayin da take ciki sosai ta fahimci ita taji abin da ya ji a jikinsa sosai ya gane haka murmushi yayi kafun ya ce.
"Magana nake yi fa ko akan Mu'azzam din masa sai an yi halin rashin son maganar?".
Ya fadi har lokacin fuskarsa akwai murmushi ita ma wani yaƙe ta dauko ta daurawa fuskarta a tunaninta wai murmashi ta mai da masa kafun ta kokarta motsa laɓɓanta.
"Uhmm yanzu ya tashi kai kuma.ka shigo".
Ta fadi tana mai nuna kamar shine dalilin rashin yin komai akan Mu'azzam.
Ya gane in da ta dosa don haƙa ya mike a kafafunsa yana kallonta ya mika mata Mu'azzam a hankali takai hannunta ta anshe shi.
"Sai anjima".
Ya fadi yana mai shafar kan Mu'azzam dake ta faman kallonsa yaka dariya.
A hankali ya fara taka kafafuwamsa ya ficewa dag cikin dakin sosai yake jin wani irin yanayi a jikinsa sosai yake jin ranar yau a gareshi ta fita daban sosai yake jin yanayi mai zubi da wani yanayi mai armashi a jikinsa a haka har ya karasa ficewa daga cikin dakin.
Wani ajiyar zuciya ta saki tana mai lumshe idanuwanta ta bude su akan Mu'azzam wanda ya kafeta da idanu kamar yasan abin da take yi ja masa kumatu tayi ya bangale mata baki sukayi hanyar Toilet din dake cikin dakin domin gyara masa jikinsa.
*****
Tun ranar da ya hadu da Mariya ya sake jin filin duniyar rayuwarsa ya sake hargitsewa sosai yake jin ciwon da zuciyarsa take masa yana kara girma matuka gaya sosai yake hango tashin hankali mara musaltuwa na kara wanzuwa gareshi.
Juyi yake yi saman gadonsa lafiyayye wanda yaji kayan shimfida amma duk da wannan taushin gadon da laushi da yake dashi hakan bai hana shi jin sa kamar akan ƙaya yake kwance ta take faman sassoke shia ko wani sashi na jikinsa.
Bai sa mai ya dace ya yi ba, Bai san abin da ya kamata ace ya aikata ba domin ceton kansa, sosai yake jin kwanyarsa ta toshe gabadaya tunaninsa ya daina kawo masa abin kirki na a zo a gani.
Zuciyarsa sosai yake jin tana kara ciwo mai girma a cikin filin ta sosai yake jin zafi da raÉ—aÉ—i a duk sakan sosai yake tsoron abin da zai faru dashi nan gaba in har zuciyarsa ba ta saman masa mafita ba sosai yake hango rayuwarsa gajarcewa take yi a duk sakan...
handle din kofar dakinsa da yaji an kama ya sanya shi saurin buÉ—e idanuwansa da suke kulle yana.jin tunanin da yake ta faman yi na kanzon kurege ya tsaya cak!.
Mu'iz ne ya shigo fuskarsa kawai zaka kalla ka gane akwai abin dake damunsa yanayin kallon da yake wa Huzaif zai tabɓatar maka akansa yake samun damuwa a filin zuciyarsa.
"Ban san wata irin rayuwa kake kokarin rakitowa kan ka ba, Ban san mai yasa kake kokarin sanyawa kan ka abin da zai hanaka walwala a duniyarka ba, Ban san mai yasa ka kasa kokari wajan yaki da abin dake damunka ba?".
Mu'iz ne yake fadin haka muryarsa cike da damuwa hannunsa harɗe a jikinsa ya jingina a kofar dakin ba tare da ya karo cikin dakinsa amma idanuwansa masu ciƙe da damuwa suna kan Huzaif dake ta faman juyi kan gadon gabadaya lokaci guda ya hargitsa shimfidar gadon.
A hankali Mu'iz ke takowa saman kafafuwansa jikinsa na bayganar da yanayin sanyi da halin da abokin nasa yake ciki a haka ya iso bakin gadon ya zauna yana kallons sosai kafun ya kai hannunsa ya ja babban bargon da ya lullube kansa dashi jikinsa daga shi sai Boxer da singilet murÉ—anÉ—an jikinsa mai cike da kirar mazantaka sosai ya bayyana kau da kai Mu'iz yayi ganin yarda da yake ciki.
"Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai ka dauki rayuwa ba ban san mai yasa kake daukar abu da girma ba wanda bai dace sam ace hakan ba haba Huzaif mana".
Ya fadi da rarrashi a muryarsa a hankali yake jan numfashi yana ajjewa kafun ya numfasa.
"ji ka don Allah a hakan kake tunanin zaka cigaba da zama a Huzaif din da a ka san ka, haka kake tunanin zaka samu walwala a rayuwarka ba tare da kayi maganin abin da ke damun ka ba kana tunanin wannan halin da ka jefa kan ka zai maka maganin matsalarka kayi ganganci Huzaif...ba ma wannan ba sosai nake mamaki Huzaif da har zaka kasa fada min abin dake damun ka nayi mamaki a zuciyata yanayin da ka nuna ace abu na damunka amma a matsayina na abokinka shakiki amma ka kasa sanar dani gaskiya bakayi ABOTA adalci ba dake tsananinmu".
Numfashi ya ja mai zafi kafun ya ciza laɓɓansa.
"Ka tashi ina son magana da kai in kuma bani da wannan matsayin sai naji in san in da dare yayi mani".
Yanayin yarda yayi maganarsa da muryarsa mai zurfi da zafi a cikinta ya sanya Huzaif motsawa yana faman cizon laɓɓansa a hankali ya ja jiki ya riko hannun Mu'iz.
Da sauri Mu'iz ya kalle shi hawaye ya gani suna sauka a idanun Huzaif da sauri ya ware idanu ya na kallonsa yana mai kara rike hannunsa sosai.
"Haba mana Huzaif! me nake shirin gani haka wai shin meke damun ka ne haka wai kuwa kasan yarda kake kuwa kana kallon kanka a MADUBI kuwa ka ga halin da ka jefa kan ka Huzaif Hawaye Huzaif hawaye a idanun ka By God Sake don Allah karka ce mani abun har ya kai haka kar kace mani matsalar da kake ciki har ta kai matakin da zaka zubda mata da hawaye...Yaa Allah!".
Janye hannunsa yayi daga na Huzaif sosai yake ware idanunwasa yana jin yarda gabansa ke bugawa cikin wani irin mataki mai girma.
"Ban san abin dake damu na ba, Mu'iz abu daya na sani Mariya ita ce ta dalilinta komai...".
"Mariyaa!"
Mu'iz ya fadi muryarsa da sauti sosai a cikinta da mamaki yake duban sa cikin wani irin yanayi wanda shi kansa bai san yarda zai fassara shi ba.
"WACECE ITA?".
Mu'iz ya fadi muryarsa da zurfi a cikinta yana mai kallon Huzaif da izuwa lokacin hawayen da yake zubda sun tsaya illa numfashi mai girma da yake ta faman ja kamar zai kufce masa.
"Ban san ya akayi kudin ƙaddara ya rakito mani ita ba ban san mai yasa kaddara ta kinkimomin ita ba ta jeho cikin rayuwata ba sosai nake cikin tashin hankali mai girma Mu'iz ban san ya zan kwatatta maka yanayin da nake ji a zuciya ta ba abu ne mai girma nake jinsa ya samu gurbi a filin zuciyata wanda ban san menene ba ban taba jin irinsa ba koma.na taba ji ban taba jin mai girma kamar wannan ba".
Zuciyar Mu'iz ce ta buga a hanzarce har sai da ya kai hannunsa ya dafe kirjinsa tsayin mintina masu auki kafun ya ja numfashi mai zafi ya fesar ya dubi Huzaif da yayi shiru numfashin sa sai kai kawo yake yi a hankali
'U'r in Love'.
Mu'iz ya fadi a zuciyarsa da wani murmushi mai girma a fuskrsa kafun ya nisa.
"Tashi ka zauna ka bani labarin yarda abun ya kasance".
Mu'iz ya fadi fuskarsa da murmushi yana mai bubbuga bayan Huzaif sakato yayi Huzaif din yayi ganin yarda Mu'iz ya nuna masa a hankali ya ja jiki ya tashi ya zauna tsakiyar gadon har da tankwashe kafafuwansa hannayensa tallabe da haɓa ya warsa idanuwansa kan Mu'iz da shima idanuwansa na kansa sun shafe fiye da mintina goma a haka kafun Mu'iz yayi kokarin kau da shirun.
"Bani labari mana Huzaif".
Ya fadi yana kafe shi da idanu
Sosai Huzaif ke kallonsa gabadaya ya rasa inda Mu'iz ya nufa sosai maganganunsa suka rikita shi ya rasa ina zai ajje su ya rasa ina suka nufa sai faman sauke ajiyar numfashi yake yi yana kallon Mu'iz
"Ban gane ba Mu'iz me kake nufi".
Ya tsine fuska yayi kafun ya gyaÉ—a kai.
"Bani labarin wacece Mariya".
tsura yayi da idanu yana tunanin mai zai ce da Mu'iz ta yaya zai ba shi labarin Mariya mai zai ce masa ya hada su kai ya shiga girgizawa yana cizon laɓɓansa a hankali shiru ya shiga tsakanknsu kafun ya kokarta sanar da Mu'iz yarda ƙaddararsa ta watso masa Mariya cikin duniyar rayuwarsa take kokarin rikita masa komai da komai.
"Yaa Allah!".
Mu'iz Ya fadi yana mai girgiza kai cikin wani irin yanayi wanda Huzaif ya kasa gane in da hakan ya dosa.
"Ban san mai yasa kake haka ba ban san mai yas kake rayuwa haka ba ban san yaushe zaka yi wayo ba a rayuwarka ba ban san mai yasa kake daukar rayuwar duniya a abun azo a gani ba".
Kau da kai Huzaif yana mai yatsine fuska don ya lura da inda maganganun Mu'iz suka dosa.
"Mtss".
Ya ja dogon tsaki kafun ya dubi Mu'iz a karo na ba a dadi.
"ni ba abin da nake bukata ba kenan so nake ka samo mani mafita ba wai wani zance na daban ba".
"tsiya ta da kai kenan Huzaif ya kamata ace ka fuskanci rayuwa tun yanzu kai ga ka da son yin abu amma sam abin bai yi maka kyau".
Cikin rashin fahimta yake kallonsa yana nazarin kalamansa.
"Na rokeka ka rabu dani Pease I don like this at All wallahi ya kamata ace ka gane ni sosai izuwa wannan lokacin...Mtss".
"Huzaif you sport to no u'r in love...Yaa Allah abu kamar almara ban san ya zan fassara maka ba halin da kake ci amma dai akwai alamun so tattare da kai...".
Ihu Huzaif ya fadi yana mai kaiwa Mu'iz wani wawan naushi a fuska da sauri ya kau ce cikin hanzari yana mai tashi daga kusa dashi cikin yanayin mamaki da kuma murmushi a fuskarsa shi dama ya san sa haka ta faru.
"U'r so stupit Mu'iz baka da hankali wallahi na lura kana hauka sosai Yaa Allah ni kake wa wannan maganar kan uban ce...".
Wani sarawa kansa yayi da sauri ya sanya hannu ya dafe yana mai yatsine fuska yana jin yarda zuciyarsa ke raÉ—aÉ—i da zafi.
"Please I beg u in the name of Allah to leave me alot I don't wanna see you please and please...".
Kansa ne ya sake dauka wata irin jiwa yaji tana sama da kasa dashi da sauri ya koma ya kwanta yana tattare jikinsa waje daya kamar mai jin sanyi sosai yaji numfashinsa na kokarin kwace masa wani irin tashin hankali yana zuciyarsa ta bankado masa lokaci guda gabadaya yaji duniyar na sukuwar doki dashi sosai yake hango tashin hankali ta yaya hakan za ta faru ta yaya Mu'iz zai kawo masa wannan mahaukacin tunanin nasa ya fada masa yace hakan ce take faruwa dashi ina! ba zai taba yuwuwa ba ai wannan hauka ce da rashin hankali kamar shi Huzaif ace wai son ta yake yi kaicon wannan mummunar labari.
Wata irin zabura yayi ya dire daga kan gadon ya isa gaban Mu'iz dake tsaye kamar wanda aka dasa mamaki ne ya cika shi ganin yanayin da Huzaif ya nuna game da maganar da yayi masa wanda in da yasan haka ce zata faru ba zai fada masa ba.
wuyar rigarsa da yaji an shaƙa ya sanya shi katse tunanin da yake yi da zuciyarsa.
"Ban san baka da hankali ba sai yau, Ban san kwakwalwarka ba ita kadai bace akan sai yau, ni zaka kawo wa wannan takaicin da bakin cikin rayuwata ashe dama ba so na kake ba ashe dama zaman tsana muke yi tsakanina da kai Well..Well ban yi mamaki ba Mu'iz dama ance makashinka yana nan tare da kai ba tare da ka sani ba yau ka nina min true colour din ka kuma na gani".
Yanayin yarda yake maganar zai tabbatar maka ba ya cikin hayyacinsa idanunsa gabadaya sun canza kamar ba nasa ba sosa jikinsa ke rawa hakan da Mu'iz ya gani ya tabbatar masa Huzaif ba ya cikin natsuwarsa yake wadannan sambatun masu kama da mai hauka tubaran dole yayi masa zuri'a domin ba ya cikin tunaninsa a hankali ya sa hannunsa ya zare na Huzaif dake wuyansa a hankali ya ja shi ba tare da gardama ba har ya isa dashi kan gadon ya kwantar dashi yana mai jama masa bargon ya lullubeshi sosai jikinsa ya wanzar da wani irin zafi sosai yana faman karkarwar sanyi sai jan numfashi yake yi da sauri sauri
Post a Comment (0)