BAYANIN AURE DA SAKI DA MAJIƁINTANSU 08


BAYANIN AURE DA SAKI DA BIKO DA ZIHARI DA LI'ANI DA KHUL'I DA SHAYARWA.

Fitowa ta 008

Ci gaba da Bayani daga inda muka tsaya,: Ana yin Raddin Mace(wato a ce an fasa auren Mace a dawo da kudin da aka bayar na Sadaki da Sauransu)
     Saboda wasu dalilai kamar haka, da kukurta da ruwan Dumi, wato kukurta mai kunkumbura fuska, da cutar Farji, kamar kashi a Farji da sauransu. Idan Mijin ya riga yayi Khul'i da ita bai sani ba, to sai ya ba ta Sadakinta, Sannan ya je wajen Ubanta ya karba abin sa, haka nan idan dan'uwanta ne ya Aurar da ita, sahihi ma sai ya biya Mijin Sadakinsa da ya bayar, amma idan waliyyi ne Wanda ba ya cikin dangi ya Aurar da ita, toh ba zai biya komai ba babu abinda za'a ba ta sai rubu'in (1/4) na dinare.

Ana jinkirtawa mara lafiyar Zakari har zuwa shekara daya domin ya Nemi Magani, idan ya warke ya iya Saduwa da Matar a shekarar shikenan,
    Idan kuwa bai warke ba sai a Raba Auren a tsakanin su, idan kuma ta yarda ta ce ita tana sonshi a haka zata zauna dashi, shikenan sai a barta, Wanda ya 'Bata kuwa aka daina ganin sa, Ana deba masa ajilin shekara hudu ne daga ranan da ta kai Maganar gaban Hukuma, in an gama bincikensa a duk inda ake tsammanin za'a same shi, ba'a same shi ba, sai a yanke mata wannan hukuncin, sannan sai ta yi idda irin iddar da Mace takeyi Na Tabaka, in ta gama Sannan ta yi Aure idan ta dama, amma ba za'a gaji dukiyarsa ba har sai bayan wani Zamani mai tsawo wanda ake hasashen cewa ba zai Kai wannan Zamanin a Raiye ba, (misali kamar idan a lokacin da ya 'Bata yana da shekara Arba'in da Haihuwa, toh sai a deba masa Kimanin shekara Saba'in ko Tamanin wato za'a deba masa sheKara 30/40. Sannan sai a kaddara ya Mutu a raba gadonsa)

An haramta Neman Mace a cikin idda, amma babu laifi a yi hannunka mai sanda da kyakkyawan zance Wanda Shari'a ya yadda dashi, Wanda ya Auri Budurwa, toh yana da damar ya zauna a wajen ta a Dakinta har na kwana 7 bai je wajen Sauran Matansa ba, kaman Wanda yanada Mata sai ya Kara Aure toh haka zaiyi kafin nan yaje Dakin Uwar Gida da sauran Matan.
       Idan Bazawara ce kuwa sai yayi kwana uku a wajenta, kada ya hada 'yan'uwa biyu ta hanyar mallaka da Saduwa, idan yana so ya Sadu da daya, toh sai ya haramtawa dayan kodai ya Sayar da ita ko ya daura mata Fansa ko 'yar'uwarta da 'yarta ba su halatta gare shi ba. Ita kuma ta haramta ga iyayensa da 'ya'yansa kamar dai yadda suka haramta ta hanyar Aure______

Ku biyo mu a fitowa ta gaba in Allah yakaimu.

Daga Zauren Muslim Women Mata Zallah
WhatsApp Group.

Muhammad Tukur Jalingo
Domin Shiga Wannan Group Zaki Iya Turo Mana Da Cikakken Sunan Ki Da Jihar Ku Ta WhatsApp Number Namu Kamar Haka
08164223447.
This Group Is Only For Women Please.
Post a Comment (0)