*NASIHOHI MASU AMFANI*
📝 Rubutawa: *Sheik Aminu Ibrahim Daurawa (Hafizahullah).*
1- KADA KAYI RIGIMA DA MUTUM UKU
-Mahaifi.
-Malami.
-Shugaba.
2- MUTUM UKU DA MUTANE BASA KAUNA.
-Mai kudi marowaci.
-Talaka mai girman kai.
-Mai neman rigima bashi da karfi.
3- HALIN MANYA UKU NE.
-Yin afwa ga wanda ya zalunceka.
-KA bawa wanda ya hana ka.
-Sada zumunta ga wanda ya yanke maka.
4- KA DARAJA MUTANE UKU A DUNIYA.
1. Dattijo.
2. Malami.
3. Iyaye.
5- KA TAUSAYAWA MUTUM UKU.
1. Tsoho.
2. mace.
3. Yaro karami.
6- KADA KA MANTA ABU UKU.
1. Mutunci
2. addini.
3. Mutuwa.
7- KA TSAFTACE ABU UKU.
1. Jikinka.
2. Tufafinka.
3. Zuciyarka.
8- KADA KA DENA NEMAN ABU UKU.
1. Ilimi.
2. arziki.
3. Aljanna.
9- ABU UKU SUNA KARA IMANI.
1- Tilawal Al-Qur'ani.
2- Kiyamul-laili.
3- Azkhar.
10- ZAKA FUSKANCI MATSALA A KABARINKA IDAN KA MUTU DA ABU UKU.
1- Hakkin Wani.
2- Dabi'ar Annamimanci.
3- Hassada.
11- ABUBUWA UKU SUNA KAUDA FUSHIN ALLAH AKAN BAWANSA:
1- Istigfari.
2- Tausayawa waninka.
3- Sadaka.
12- IDAN ALLAH YA BAKA ABU UKU TO KA GODEWA ALLAH:
1- Lafiya.
2- Wadata.
3- Basira.
13- KADA KA YARDA KA AURI MACE MAI DABI'O'I GUDA UKU:
1- Mai yawan fushi.
2- Maras sirri.
3- Marar tsafta (Kazamiya).
14- KA YI KOKARI KA GINA RAYUWARKA AKAN ABU UKU:
1- Son Allah da Manzonsa.
2- Gaskiya da Rikon Amana.
3- Hakuri da Jarrabawa a Rayuwa.
15- ABUBUWA UKU KA ROKI ALLAH (S.W.T) YA TSARE KA DA AIKATA SU:
1- Yanke Zumunta.
2- Zagin Sahabbai.
3- Mutuwa da hakkin wani.
16- MUTANE UKU KADA KA SAURARI MAGANARSU:
1- Makaryaci.
2- Magulmaci.
3- Malami mai kwadayi da son zuciya.
17- MUTUM UKU KADA KA YARDA SU DINGA KUSANTARKA:
1- Munafiki.
2- Mazinaci.
3- Maras kunya.
18- ABUBUWA UKU BA A SON JINKIRTA SU IDAN LOKACIN SU YA ZO:
1- Sallah.
2- Aure.
3- Jana'iza.
19- ABUBUWA UKU RIKO DA SU YANA SAMAR DA RABO A LAHIRA:
1- Kokarin ibada.
2- Kula da Nafila.
3- Amfani da Halal a Rayuwa.
20- ABUBUWA UKU SUNA HANA MUTUM TANADIN LAHIRA:
1- Dogon Buri.
2- Rashin karanta Alkur'ani.
3- Nisantar sauraron Wa'azi.
20- MUTANE UKU SUNA SAMUN TAIMAKON ALLAH:
1- Mutumin da yake Neman aure Don ya kare mutuncin kansa.
2- Mutumin da ya tafi jihadi, Domin daukaka kalmar Allah.
3- Bawa wanda aka dora masa fansar kansa.
21- ABUBUWA UKU NASA ZUCIYA TA GURBACE:
1- Rashin yarda da kaddara.
2- Aibata bayin Allah na kwarai.
3- Wulakanta Iyaye.
Allah Yasa Mu Dace.
