MIJINA YANA SADUWA DA NI RANAR GIRKIN KISHIYATA



MIJINA YANA SADUWA DA NI RANAR GIRKIN KISHIYATA

*TAMBAYA*❓

Asslmu alaikum
Mun kasance mu biyu awajen mijinmu.
Sai ya kasance yar uwata bata iya gamsar dashi, to ko ranar girkinta yakan shigo ya tara dani da rana ko da daddare.

Tambaya anan shi ne malam shi hakan ya halasta?
Kuma idan na mishi magana yadaina zuwa baya ji ba gidan mu daya ba.
Dan Allah hukuncin hakan da mafita.

*AMSA*👇

Wa'alaikum assalam, Ya wajaba ya nemi izininta, tun da hakkinta ne, in har ta sarayar ya halatta ya sadu da ke a ranar kwananki da kwananta.
Saboda lokacin da Nana Saudah ta tsufa ta ji tsoron kada Annabi S.A.W ya sake ta, ta dauki kwananta ta bawa Nana A'isha, kamar yadda Bukhari ya rawaito. 

Bayan haka Annabi S.A.W yana yin kwana dai-dai a dakunan matansa guda bakwai, ita kuma Nana Aisha yana mata kwana biyu, Saudat kuwa ba ya kwana da ita, saboda ta sarayar da hakkınta.

Allah ne mafi sani.

Dr. Jamilu zarewa.

Ku kasance damu domin ilimintarwa da Fadakarwa da Tunatarwa a Sunnah.
KU BIYOMU A TELEGRAM:👇
https://t.me/TambayoyiDaAmsoshi
KU BIYOMU A FACEBOOK👇
Https://www.facebook.com/groups/336629807654177
Post a Comment (0)