TAΖARGAZARSU GA ALI (RA)
A cikin ΖoΖarinsu na Ιata sunan shugabannin Musulunci da siffanta su da siffar marasa mutunci, malaman Shi’a suna dangana maganganu masu yawa ga Sarkin Musulmi Ali binu Abi Ζalib, Allah ya Ζara masa yarda, irin maganganun da ba mai furta su sai wanda ya kai matuΖa a rashin mutunci. Babban malaminsu mai suna Muhammad BaΖir Almajalisi ya ruwaito cewa: Wata mace ta miΖe a cikin masallaci, alhalin Sayyidina Ali yana yin huΙuba, sai ta ce, “Ya kai makashin masoya!” Wai sai Sayyidina Ali ya dube ta, ya ce: “Ya ke mara kunya, ya ballagaza. Ya wacce ba ta haila kamar yadda mata ke haila. Ya wacce a kan abin naninta akwai wani abu da ya burtso, yana reto.” *[Duba Biharul Anwari na Muhammad BaΖir Almajalisi, bugun Ihiya’ut Turathi, Bairut, 1403, mujalladi na 41, shafi na 293].* “ABINNANI,” wannan fassarata ce, amma shi mai ruwayar ya yi amfani da wata kalmar Larabci da take nufin FARJI, wacce idan da za mu fassara ta zuwa Hausa to da sai dai mu koma ga tsohuwar Hausa ta Maguzawa mu nemo kalmar.
Saboda Allah, ya Ιan uwa mai karatu, tana yiwuwa Ali binu Abi Ζalib, Allah ya Ζara masa yarda, ya furta waΙannan kalmomi, alhali yana kan mimbari yana huΙuba a masallaci? Kuma idan ya yi nufin ladabtar da wannan matar ne, ko mayar mata da martani, babu wasu kalmomin da suka fi dacewa da matsayinsa na Sahabi, kuma Ζanin Annabi (SAW), wanda ya taso aka raine shi a gidan Annabta? Babu shakka wannan ΖoΖarin Ιata sunan Ali ne, da ma sauran Ahalul Baiti, da Ζ΄an Shi’a suke yi, kuma a lokaci guda suna fakewa (suna yin TaΖiyya) da cewa wai su masu Ζaunar su ne.
Har yau, akwai wani labari da Ζ΄an Shi’a suke bayarwa cewa, wai wata rana wata mace ta yi wa wani mutum Ζazafi, sai ta Ιauki ruwan Ζwai farin, ta zuba shi a tsakanin Ζafafunta, ta ce wai ya yi lalata da ita, kuma wannan maniyyinsa ne. Wai sai Ali binu Abi Ζalib (RA) ya tashi, ya duba tsakanin Ζafafunta, ya ce Ζarya take yi, wannan ba maniyyi ba ne!! *[Duba Biharul Anwari na Majalisi, mujalladi na 4, shafi na 303]* .
Mai karatu, sai ka duba wannan magana da idanun basira. Ta ΖaΖa Ali zai duba tsakanin Ζafafun mace muharrama don kawai ya tabbatar da Ζarya ko gaskiyarta?! Shin duka garin ba wata mace wacce za’a sa ta yi wannan aikin? Shin wannan ba ΖoΖarin zubar da mutuncin Sarkin Musulmi Ali ba ne?
*TaΙargazarsu Ga Nana FaΙima (RA)*
Malaman Shi’a sun siffanta Nana FaΙima, Allah ya Ζara mata yarda, da siffofi waΙanda suke nuna matuΖar suka da zubar da girma. A nan ma, za mu taΖaita saboda munin waΙannan siffofin.
A dangane da gadonta da suka ce wai Khalifa Abubakar SiddiΖ ya hana ta, kuma wai Umar ya Ιaure masa gindi a kan haka, suna ruwaito yadda ita FaΙima Ιin ta kai gwauro ta kai mari don neman gadon nata. Suka ce, “FaΙima(AS) ta iske Abubakar da Umar a masallaci, ta yi musu maganar gadonta na gonar Fadak, inda ta yi faΙa da su, ta yi kururuwa, mutane suka taru, kuma ta kama wuyan Umar ta jawo shi zuwa gare ta.” *[Duba Kitab Salim binu Ζais na Salim binu Ζais Alhilali, bugun Mu’assasatul Bi’itha, Bairut, ba tarihi, shafi na 253].*
Mai karatu ya dubi yadda wannan ruwaya ta siffanta FaΙima: matar aure, Musulma, ta iske mazaje, abokan ubanta (kuma surukansa), a bainar jama’a, ta yi faΙa da su a kan gona, har ta ci kwalar Ιayansu!! Shin idan ma wannan gadon ya dame ta, ba ta da miji, ko wani Ιan uwa, da zai karΙo mata haΖΖinta? Ai ba FaΙima ba, wacce take Balarabiya, BaΖuraishiya, Bahashima, kuma Ζ΄ar Manzon Allah(SAW), ko wata Ζ΄ar Fulani Bakanuwa, ba za ta aikata wannan rashin mutuncin ba. Amma abin mamaki shi ne, Ζ΄an Shi’a sun yarda da wannan ruwaya, kuma suna kattaba ta a cikin littafansu!!
Irin waΙan nan maganganu na Ιatanci da Ζ΄an Shi’a suke dangana wa Ahalul Baiti suna da yawa ainun a cikin littafansu. A nan, mun kawo Ιan misali ne kawai don mu tabbatar wa da mai karatu cewa da’awar Ζaunar iyalin gidan Manzon Allah(SAW) da Shi’awa suke yi munafurci ne kawai da yaudara da TaΖiyya!!
*- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 3: "AΖidar TaΖiyya a wajen Ζ³an Shi’a" - na Prof. Umar LabΙo*
*✍ AnnasihaTv*
*- Ga masu son siyen littafan da ma wasu littafan Prof sai su tuntuΙe mu kamar haka;*
*Call/WhatsApp:* 08142286718
*Twitter:* https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09
