WANDA YA SAKI MATARSA A ZUCI BATA SAKU BA

*WANDA YA SAKI MATARSA A ZUCI BA TA SAKU BA!*
*TAMBAYA:*
Assalamu Alaikum,
Don Allah Malam, idan mutum da dare ya qudurta zai saki matarsa zuwa safe, amma bai furta ba zuwa safiyar kuma sai ya canza shawara. Shin yaya matsayin auren yake?
Allah Ya taimaka.
*AMSA:*
Wa alaikumus assalam, Mutukar bai furta ba kuma bai rubuta ba to Ba ta saku ba, saboda Allah ba Ya kama Al'ummar Annabi Muhammad S. A. W. da zancen zuci kamar yadda hadisi ingantacce ya tabbatar.
Allah ne mafi sani.
Amsawa:
*_Dr Jamilu Yusuf Zarewa_*
01/08/2017.

Post a Comment (0)