JINJINA DA YABO GAREKI, BISA AIYUKKA NA JINΖAI,
ALLAH ΖARA RIΖO DA HANNUNKI FAUZIYYA D. SULAIMAN.
Ya mafi iya saka khairi,
Ka yi sakamakonKa tari,
Kariya daga dukka sharri,
Ζaukaka da rufin asiri,
Ζara yi wa Fauziyyar nan.
Allah Baiwarka ga ta,
Fauziyyar Marubuta,
Mai jinΖan mabuΖata, da
Garkuwar yara da mata,
Inuwa ta shiga su huta,
Yi jibintar lamuranta,
Har ma da gidauniyarta,
Ζarfafa guiwa gareta,
Yi daΙin buΙi, wadata,
Ζara yauΖaΖa arziΖinta,
DaΙa tsarkake zuciyarta,
Ya Allah Ka tsare ta,
Ga duk sharrin magauta,
Da shiga komar macuta,
Kar sui nasara a gun ta
Janye sheΙanu jikinta,
Ka tsaya mata kai-da-fata,
A cikin duk lamuranta,
Masu son su ga tawayarta,
Ko Ιacin ayyukanta,
Kar sui nasara a kan ta,
Yi daΙin shiriya a gunta,
Ta fi Ζarfin zuciyarta,
Darajarta ka Ιaukakata,
Ζara albarka gareta,
Kyawun Ζarshe Ka bata,
Da shahada Ιauki ranta,
Aljanna ciki ka sa ta,
Ka yi jinΖan walidanta,
Albarkaci zuri'arta,
Bayanta ka kyautata ta,
DaΙa kyakkyawar fahimta,
Da uban 'ya'ya mijinta,
So da Ζauna ka daΙe ta,
Da biyayyar Annabinta,
Don isar mulkinKa Amin.
