TAMBAYA TA 54

TAMBAYA ======== 👇 Assalamu alaikum Barka dawar haka malam ya ayyuka da iyali dafatan komi lahiya. Malam jiya wata cousin Dina tazo take tambayata wai taji wani wa'azi malamin nabayani akan duba . Yanacewa inhar mutum zeyi dubane akan sonsanin wani al amari Wanda baidanganci cutarwa ba balefi. Sannan yakawo misali Wai a zamanin sahabbai ma sunyi duba Dan sugane wani al amari daya kulle Kansu. Dan Allah malam micece gskyr al amarin AMSA ====== 👇 Tabbas manzon Allah saw ya bayyana mana cewar, daga karshen zamani Allah zai dauka ilimi ta hanyar mutuwar Malamai, daga karshe sai mutane Su riki jahilai suna neman FATAWA a wurinsu, Su kuma suna basu FATAWA ba tare da ilimi ba, Su masu Bada fatawar Sun bata kuma sun batar da wadanda suka nemi FATAWA a wurinsa. Hakika wannan hadisin ya fara aiki akan wannan malamin. Yanzu abinda muke jira kuma, ki koma wajen wannan malamin ko ki aika masa tambaya ta hanyar radio in a radio kika saurareshi, sai ya sanar damu inda sahabbai sukayi duba, tare da cikakken dalilai. Allah shine masani. ✍ ZAUREN FADAKARWA A SUNNAH MAZA MATA 08108605876
Post a Comment (0)