♡... MAIRO ...♡*
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*25*
*_Saturday morning..._*
_8:24am_ Qasin ya shigo part ɗin momi cikin kananan kaya,
parlour ya tararda su suna karyawa.
momi na ganinshi gabanta ya faɗi a haka ta ɗaure ta amsa gaisuwar da yayi mata "lafiya kalau ya naganka cikin shiri haka?"
yan duba agogon hannunsa yace "wlh meeting ne wai zamuyi da wasu kuma basu faɗa min ba sai jiya da maraice gashi anjima zasu wuce balle nayi cancle ɗinshi"
wani daɗine ya jiyarci zuciyar mairo da momi mairo kasa jurewa tayi saida tayi dariya,
cup ɗin tea momi ta aje mishi "xauna ka karya mana"
ɗaukar tea yayi a tsaye yana sha "bani da time ɗin tsayawa ina Siraj ne?"
"yaje birnin kebbi"
fuskar mamaki yayi birnin kabbi gurin mie?"
"nima ban saniba baba hajara ce ta aiko tana nemansa tun da 7 ya tafi"
iskar bakinsa ya busar "owk maryam tashi ki chanja kaya ki rakani"
da sauri momi ta kalleshi "gurin meeting ɗin zata rakaka?"
"eh momi ban yarda da barinta cikin gidan nan ba"
faɗa momi ta taso masa dashi "tho bazata ba in baka yarda da magana naba sai kayi abunda zakayi nifa na haifeka Qasin ba ni ka haifa ba"
kasa yayi da kansa yana sauke ajiyar zuciya,
duk sai yaji ba daɗi ganin yadda ranta ya bace haka ya juya jiki ba kwari ya fice.
*_9:41am..._*
motar Yarima tayi parking,
ya kusan minti uku ciki motar sannan ya fito ya nufi parlour.
da sallama ya shigo mairo ta amsa masa tana murmushi,
tsaye yayi yana kare mata kallo ganin yadda tayi masa mugun kyau doguwar rigace jikinta golden colour sai ɗan karamin bakin hijab da momi ta saka mata da da jan janbaki sosai tayi kyau,
a hankali ya karaso kusa da ita ya risina ya kai hannu ya taɓa gefen fuskarta yana haɗiye yawu,
murmushi ta sakar masa "ina kwana"
bai amsa mata ba
ya mayar mata da murmushin yana mata wani kallo,
jin an taɓa kofa ya sashi tashi ta sauri ya matsa baya yana kallon momi data nufo downstairs.
"Yarima ka iso?"
"eh momi naga har kin shiryata"
"eh kasan kace mun 9:30 zaka zo"
agogon hannunsa ya kalla "bari muje momi kar muyi african time"
"owk tho Allah ya kiyaye"
hannunta ya rika suka fice tana yiwa momi byebye.
murmushi momi ta bita dashi har ta fice ko kaɗan momi bata son tafiyarta dan dai babu yadda zatayine tunda tana ganin inta hana mairo zuwa bata kyautawa Yarima ba,
'''*************'''
Qasin ne tsaye tsakiyar ɗaki yana kai da kawo kana ganin yanayin fuskarsa kasan ransa a bache yake.
momi ma zaune take saman kujera dafe da kai lokaci lokaci takan kai dubanta gurin agogon dake parlour.
wannan karon *9:21pm* ya nuna hankalinta ne ya kara tashi,
da sauri ta janyo wayar dake hannunta tana kiran number Yarima duk sakamoko ɗaya ake bata kamar ɗazun wayar a kashe,
juyowa Qasin yayi ya kalleta "kinga ni ko momi saida nace miki karki barta taje kika ki yarda da magana na gashi yanxu abunda ake yiwa gudu"
numfashinsa momi ta tara "babu abunda zai samesu insha Allah kawai dai bana son sukai 10 ne"
magana take kamar abun bai dameta ba saɓanin cikin ranta dake cike da tashin hankali,
kai Qasin ya girgiza "hmm ace tun safe mutun ya fita har yanzu babu labarinsa"
da karfi Mairo ta turo kofar parlour ta shigo idonta zurun zurun.
duk juyowa sukayi suna kallonta babu wadda ya iya taɓuka komai harta karaso kusa dasu,
lumshe ido Qasin yayi yana sauke ajiyar zuciya.
da fata momi tayi tana kallon bayanta "ina Yarima?"
"yana can basan inda yake ba sawa yayi a kawoni"
magana take muryarta na rawa kana gani kasan tsoro take ji sai waiga bayanta take,
juyowa Qasin yayi da ita "maryam mi yasa kuka daɗe?"
shiru tayi tana haɗiyar yawu "ba ba babu komai"
tsawa Qasin ya katsa mata yana girgiza ta "faɗamin min gaskiya tun safe ku fita sai yanzu ki dawo kice mun babu komai faɗa min miya faru?"
matsawa tayi ta rike momi tana kuka "yace duk na faɗa sai ya kasheni"
sanyi jikin Qasin yayi momi kuma tsigar jikinta ta tashi,
a hankali momi ta rika zata zaunarda ita kin zama mairo tayi ta ɗan ɗaga rigarta cike da tsoro tace "momi kayana duk ya ɓata dubi jini na min zuba"
da sauri Qasin da Momi suka kalli jinin dake bin k'afarta.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com
*BY*
*_KHADEEJA CANDY_*
*25*
*_Saturday morning..._*
_8:24am_ Qasin ya shigo part ɗin momi cikin kananan kaya,
parlour ya tararda su suna karyawa.
momi na ganinshi gabanta ya faɗi a haka ta ɗaure ta amsa gaisuwar da yayi mata "lafiya kalau ya naganka cikin shiri haka?"
yan duba agogon hannunsa yace "wlh meeting ne wai zamuyi da wasu kuma basu faɗa min ba sai jiya da maraice gashi anjima zasu wuce balle nayi cancle ɗinshi"
wani daɗine ya jiyarci zuciyar mairo da momi mairo kasa jurewa tayi saida tayi dariya,
cup ɗin tea momi ta aje mishi "xauna ka karya mana"
ɗaukar tea yayi a tsaye yana sha "bani da time ɗin tsayawa ina Siraj ne?"
"yaje birnin kebbi"
fuskar mamaki yayi birnin kabbi gurin mie?"
"nima ban saniba baba hajara ce ta aiko tana nemansa tun da 7 ya tafi"
iskar bakinsa ya busar "owk maryam tashi ki chanja kaya ki rakani"
da sauri momi ta kalleshi "gurin meeting ɗin zata rakaka?"
"eh momi ban yarda da barinta cikin gidan nan ba"
faɗa momi ta taso masa dashi "tho bazata ba in baka yarda da magana naba sai kayi abunda zakayi nifa na haifeka Qasin ba ni ka haifa ba"
kasa yayi da kansa yana sauke ajiyar zuciya,
duk sai yaji ba daɗi ganin yadda ranta ya bace haka ya juya jiki ba kwari ya fice.
*_9:41am..._*
motar Yarima tayi parking,
ya kusan minti uku ciki motar sannan ya fito ya nufi parlour.
da sallama ya shigo mairo ta amsa masa tana murmushi,
tsaye yayi yana kare mata kallo ganin yadda tayi masa mugun kyau doguwar rigace jikinta golden colour sai ɗan karamin bakin hijab da momi ta saka mata da da jan janbaki sosai tayi kyau,
a hankali ya karaso kusa da ita ya risina ya kai hannu ya taɓa gefen fuskarta yana haɗiye yawu,
murmushi ta sakar masa "ina kwana"
bai amsa mata ba
ya mayar mata da murmushin yana mata wani kallo,
jin an taɓa kofa ya sashi tashi ta sauri ya matsa baya yana kallon momi data nufo downstairs.
"Yarima ka iso?"
"eh momi naga har kin shiryata"
"eh kasan kace mun 9:30 zaka zo"
agogon hannunsa ya kalla "bari muje momi kar muyi african time"
"owk tho Allah ya kiyaye"
hannunta ya rika suka fice tana yiwa momi byebye.
murmushi momi ta bita dashi har ta fice ko kaɗan momi bata son tafiyarta dan dai babu yadda zatayine tunda tana ganin inta hana mairo zuwa bata kyautawa Yarima ba,
'''*************'''
Qasin ne tsaye tsakiyar ɗaki yana kai da kawo kana ganin yanayin fuskarsa kasan ransa a bache yake.
momi ma zaune take saman kujera dafe da kai lokaci lokaci takan kai dubanta gurin agogon dake parlour.
wannan karon *9:21pm* ya nuna hankalinta ne ya kara tashi,
da sauri ta janyo wayar dake hannunta tana kiran number Yarima duk sakamoko ɗaya ake bata kamar ɗazun wayar a kashe,
juyowa Qasin yayi ya kalleta "kinga ni ko momi saida nace miki karki barta taje kika ki yarda da magana na gashi yanxu abunda ake yiwa gudu"
numfashinsa momi ta tara "babu abunda zai samesu insha Allah kawai dai bana son sukai 10 ne"
magana take kamar abun bai dameta ba saɓanin cikin ranta dake cike da tashin hankali,
kai Qasin ya girgiza "hmm ace tun safe mutun ya fita har yanzu babu labarinsa"
da karfi Mairo ta turo kofar parlour ta shigo idonta zurun zurun.
duk juyowa sukayi suna kallonta babu wadda ya iya taɓuka komai harta karaso kusa dasu,
lumshe ido Qasin yayi yana sauke ajiyar zuciya.
da fata momi tayi tana kallon bayanta "ina Yarima?"
"yana can basan inda yake ba sawa yayi a kawoni"
magana take muryarta na rawa kana gani kasan tsoro take ji sai waiga bayanta take,
juyowa Qasin yayi da ita "maryam mi yasa kuka daɗe?"
shiru tayi tana haɗiyar yawu "ba ba babu komai"
tsawa Qasin ya katsa mata yana girgiza ta "faɗamin min gaskiya tun safe ku fita sai yanzu ki dawo kice mun babu komai faɗa min miya faru?"
matsawa tayi ta rike momi tana kuka "yace duk na faɗa sai ya kasheni"
sanyi jikin Qasin yayi momi kuma tsigar jikinta ta tashi,
a hankali momi ta rika zata zaunarda ita kin zama mairo tayi ta ɗan ɗaga rigarta cike da tsoro tace "momi kayana duk ya ɓata dubi jini na min zuba"
da sauri Qasin da Momi suka kalli jinin dake bin k'afarta.
*©Khadeeja Candy*
candynovels.wordpress.com