YADDA WATA MATA TA HANA MIJINTA SHAN SIGARI

✴✴✴✴✴✴✴✴✴✴✴✴
*ABOKIN FIRA �*
*Rubutawa:* _Dr. Muhammad Mansur Sokoto_

*DRS NA 018*

*Yadda Wata Mata ta Hana Mijinta Shan Sigari*
Wata mata. Rannan sai ta yi tunanin hanyar da za ta yi masa wa’azi ba tare da ya samu wata kafa da zai yi mata gardama ba.
Watarana suna zaune sai ya dauko karen sigarinsa zai kunna, a cikin raha sai ta tambaye shi, nawa ake sayar da karen sigari guda daya? Sannan kuma guda nawa yake sha a wuni? Da ya ba ta amsa sai kuma ya kara da cewa, ko kina so ke ma ki fara sha ne? Sai ta ce masa
a’a. Amma dai ni a matsayina na iyalinka akwai abin da nike sha’awar in saya ba sigari ba. Ba tare da jin wata damuwa ba ya yanka mata
kudin da zai rika ba ta a madadin sigari da yake sha.
A kwana a tashi yana ba ta kudi duk safiya ashe matar nan tana
ajiye kudin nan har suka taru suka yi yawa sosai. Rannan sai ta aika aka canjo mata su aka kawo mata sababbin kudi daga banki. Suna zaune suna fira sai ta fito da kudin, kamar da wasa sai ya ga ta dauko ashana za ta kyasta masu. Gogan naka sai ya rike hannunta. Ba ki da hankali ne? A cikin sassaukar murya sai ta ce masa, ba ka san ko kudin me ne ba? Ya ce, ko ma na mene ne ya za ki kona su? Ta ce, ai kudin sigarina ne da kake ba ni. Ni ma yau zan kona su gaba daya. Nan take
sai jikinsa ya yi sanyi, ya fara ba ta hakuri. Sai ta ce da shi ka ga ni yanzu ko na kona wadannan kudin baa bin da zai same ni. Amma kai a
duk safiya ta Allah sai ka kona kudinka a cikin kirjinka kana sanya ma kanka cuta wadda a nan gaba ni ne zan zama mai jinyar ka a kan ta. In takaice maku labari dai da haka wannan mata ta shawo kan mijinta ya daina shan sigari, aka zauna lafiya. �

*Darasi:*
▶ Abin da sauki da lumana ba su kawo ba fitina da tashin hankali ba su kawo shi.

▶ Maganar gaskiya idan an fade ta yadda ta dace lalle ne za ta yi tasiri, ta yi amfani.

▶ Yadda Macce take rainon ‘ya’yanta hakanan take yi idan tana da basira ta yi tarbiyyar mijinta.

▶ Da yawa wanda yake aikata laifi amma ba ya jin girman laifinsa sai an fadakar da shi.

▶ Sabo jarabawa ce. Duk ranar da Allah ya dauke ma bawa shi sai ya yi masa mafita da zai bar shi. �
📕📕📕📕📕📕📕📕📕📕📕📕📕
Email: jibwissocialmediaktlg@gmail.com
Facebook: Jibwis Katsina L.G
WhatsApp: 07062584992, 08038977817, 08034453678, 08036958490.

Post a Comment (0)