ADDUA GA YARAN MU

ADDUA GA YARAN MU



(1) Allah kayi min albarka a cikin 'ya'yana 

(2) Allah kayi masu muwafaka su zamo masu yi maka biyayya 

(3) Allah ka azurtani da suyi min biyayya   

(4)Ya Allah yadda ka sanar da Annabi Musa ilimi ka sanar da 'ya'yana ilimi.

(5) Ya Allah yadda Ka fahimtar da Annabi Sulaiman Ka fahimtar da 'ya'yana.

(6) Ya wanda Ya ba Annabi lukman hikima. Allah ka Bawa Yaya na hikima kuma ka basu iya zance.

(7) Allah Ka bawa 'ya'yana ilimin da basu sani ba.

(8)Allah Ka tunatar da su abinda duk suka manta 

(9) Allah ka budewa 'ya'yana albarkar sammai da kasa

(10) Allah Kai mai ji ne kuma mai amsawa ne.

(11) Allah ina rokonka, ka bawa 'ya'yana gam da katar .

(12) Ya Allah Ka basu karfin hadda, kuma Ka basu saurin ganewa,Ka basu kaifin tunani

(13) Allah kasa 'ya'ya na su zamo shiryayyayu, masu shiryarwa

(15) Allah Kai mai ji ne kuma mai amsawa 

(16) Allah kar Ka sauyar da Imani a cikin zukatan su.

(17) Allah Ka kawata zukatansu da Imani, Ka sa masu kyamar kafircine

(18) Allah Ka sa masu kyamar fasikanci da kyamar sabon Ka ne

(19) Allah Ka sanya su cikin shiryayyayu.

(20) Allah ka gyara halayen 'ya'yana, Ka cika zukatan su da haske da hikima.

(21) Allah ka tsarkake zukatan 'ya'ya na ga barin riya.

(22) Allah Ka tsare mani gaban 'ya'yana, Ka kare su ga yin zina,Ka kare su daga yin luwadi,Ka kare su daga yin madigo ka kare su da dukkan
laifuffuka ka kare mani zuri'a ta.

(23) Allah Ka sanya 'ya'yana su zamo mahaddatan Al-Qur'ani,su zamo masana Sunnar Annabin Ka(SAW)

(24) Allah Ka azurta 'ya'yana da kamewa da yarda da hukuncin da kayi akan su

(25) Ya Allah Ka azurta 'ya'yana da kaunar Ka da kaunar Annabin Ka da kaunar duk wanda Kake kauna da kaunar duk wani aiki da zai kusantar dasu zuwa ga samun soyayyar Ka.  

(26) Ya Allah Ka budewa 'ya'yana kofar arziki na halal daga mayalwaciyar falalar Ka kuma Ka wadatar da su da halal da barin haram.

(27) Allah ka nisantar dasu daga abokai ko kawaye munana da zasu bata tarbiyyar su ko halayen su Ka raba su da alfasha da dukkan mummunan abu.

(28) Allah kasa 'ya'yana su zama masu lafiya a jikin su, Ka kare masu kunnuwan su,Ka kare masu idanuwan su,Ka kare masu rayukan su,Ka kare masu gabbansu ga barin sabon ka ya mai jin kan masu jin kai .Amin Ya Rabbil Alamin.

DON ALLAH WANDA DUK YA SAMI WANNAN ADDUA TO YA TURAWA DAN UWA KO MU RIKA YIWA YARAN MU su zamo nagari.KUMA YA ZAMO SADAQATUL 
JARIYA A GAREMU.ALLAH YA SHIRYA MANA SU KUMA YA ALBARKACI RAYUWAR SU AMIN.
Post a Comment (0)