UKU-BALA'I 23

UKU-BALA'I
NA
KAMALA MINNA
*ZAMANI WRITERS ASSOCIATION*
​​WÉ› ɑʀɛ ɦɛʀɛ tѳ ɛɗucÉ‘tÉ›, MѳtiѵɑtÉ› ɑɳɗ ɛɳtɛʀtÉ‘iɳ ѳuÊ€ ʀɛɑɗɛʀร​.

BABI NA ASHIRIN DA UKU.
Sosai take jin maganganun Alhaji Abdulwahaab na mata kuwwa a kunne ta rasa mai yasa haka, ta rasa mai yasa zuciyarta take koƙarin dauko mata abin da bata shirya tarbarsa ba, kokari take ta kau da komai a zuciyarta wanda sam bata muradin ace sun shigo har suna ƙoƙarin sanyata wani hali Dr.Erena mutum ne da ya kama ace ta ajje komai nata ta fuskance shi sosai da sosai sannan duk wata fargaba ko SHAKKA gami da tsoro ya dace ma ace babu su a filin rayuwarta.
Nisawa tayi tana mai jan numfashi mai zafi tana fesawar wasu lamura ne masu matukar tasiri a rayuwarta taji suna dawo mata kamar yanzu ne suke fado duniyarta ji take yi kamar yanzu ƙaddara ta hadata da Dr.Erena komai taji ya sanko mata lokaci guda a zuciyart da sauri ta ja burki a gefen titi tana mai hada kanta da sitiyari zuciyarta taji tana wani lugudan bugu wasu hawaye masu tsananin zafi da kokarin yayyaga zuciya suka shiga zubo mata...
*******
*JANUARY 2004.*
*KADUNA GIDAN MARAYU.*
"Alhaji Mati ba wai ban yarda da kai ba ne, kawai dai ka san sha'ani na rayuwar a wannan zamanin sosai yara irin wadannan suke shiga kuncin rayuwa a hannun wanda suke daukar su anyi ba sau daya ba, ba sau biyu ba a nan gidan shiyasa kaga gabadaya yanzu ba ma yarda da mutane sam! da suke zuwa daukar marayu da sunan rike su wasun su da yawa ba saboda Allah suke daukar su ba su da tasu manufar akan marayun da suka dauka...".
Nisawa yayi yana kara gyara glass din fuskarsa kafun ya dubi Alhaji Mati da yayi masa kuri da idanu yana dubansa kamar zai cinye shi danye sosai yake jin zafi da raÉ—aÉ—i a zuciyarsa sosai da sosai yake jin zuciyarsa na wani irin zugi ji yake yi kamar ya tashi ya makure wannan mutumin da yake kokarin yi masa sakiyar da ba ruwa ba zai yarda ba da wannan gangancin ba ba zai lamunci wannan haukar da wannan mutumin ke kokarin yi masa ba.
Nisawa yayi yana kokarin boye bacin ran dake kokarin bayyana kansa a fuskarsa wani shu'umin murmushi ya kalato ya sauke kafun ya kau da kai yana hirji kasa-kasa.
"a zamanin nan da muke ciki da yawa marayun da ake dauka suke shiga gararin rayuwa suke shiga tashin hankali sai mutane su zo da sunan ba su da 'ya'ya Allah bai basu haihuwa ba a taimaka a ba su za su rike tamkar 'ya'yan cikin su amma daga baya bayan sun samu cikar burin su sai su canza alkibla akan 'ya'yan da aka ba su da KUDIRI da sukayi niyya a zuciyarsu ba zan boye maka ba Alhaji Mati ka ganni nan nayi kuka da idona da girmana da kake gani a haka akan tashi hankalin da marayu suke shiga a hannun masu daukar su da sunan riko ban san adadin yawan marayun da suka bata ba ban san adadin marayun da aka bata wa rayuwa ba ban san adadin marayun da aka ciwa zarafi ba ban san adadin marayu mata da aka KETA HADDI a garesu ba haka ma mazan su ma ba a bar su ba...".
Shiru yayi yana jan numfashi zuciyar na wani irin bugawa ransa na kara É“aci a hankali ya ja glass din idanunsa ya dauke wasu kwalla da suka tarun masa kafun ya sake nisawa yana duban Alhaji Mati da izuwa wannan lokaci ya kosa da dogon sharrin da yake yi masa wanda shi dai a karan kansa ba abin da suke yi masa domin bi sukeyi ta bayan kunnan sa suna wuce wa ba abin da ya kawo shi kenan a zaunar dashi ana karanta masa halin marayu ba shi zuwa yayi a bashi abin da yake bukata ko nawa ne zai biya a zuciyarsa ba wai marayu ya zo dauka ba siyar maraya ya zo yi da kudin sa domin bukatarsa ce ta taso a filin duniyar rayuwarsa.
"MARAYU MA 'YA'YA kamar ko wani ɗa a filin duniyar nan suna da gata da galihu gami da 'yanci a rayuwarsu kawai dai har yanzu ba a san wanene maraya ba duk marayu da ka ga ana ajje su a wannan gidan to in ka bincika ba su da laifin ko miskala zarratin a filin duniyar su da yawan su haihuwar su ake ana yasar da su a titi ba tare da sun sani ba da yawan su iyayen su da suka haife su ba wai ta hanyar sunna bace ake samun su ya kamata a daina ganin laifin marayu ba su suka halicci kan su ba haka ƙaddarar su ce ta zo a hakan in da suna da iko wallahi ba yarda za ayi su bar iyayensu su haife su ta wannan gurbatacciyar hanyar...abin takaici yawan mutanan mu ba sa duba ga hakan kawai yankewa maraya hukunci suke yi da bahagon tunani ya kamata ace an daina ganin laifin maraya maraya rauni gareshi maraya mai bukata ne a filin duniyarsa maraya shima ɗa ne kamar ko wani ɗa a filin duniyar nan...".
Nisawa yayi muryarsa a lokacin ta kara rauni.
"...don Allah Alhaji Mati ka dubi girman Allah da Annabi kayi mani alkawari ba zaka zamo daya daga cikin mutane da masu cin zarafin marayu ba...".
"Ba sai ka roke ni ba Uban Marayu".
Alhaji Mati ya fadi da murmushi kwance a fuskarsa kafun ya cigaba da cewa.
"Bana cikin irin wadannan mutanan masu tauye hakki har haka ka yarda dani Alkawari nayi maka ba zaka samu matsala dani ba domin nasan darajar maraya domin nima na É—anÉ—ani irin rayuwar tasa kuma ban ji dadi ba ka ga kuwa ba yarda za ayi ace na so wani dan uwa nawa ya shiga irin wannan halin".
Ya karashe da yanayin rauni a fuskarsa.
"Naji dadin haka sosai da sosai Allah yayi mana jagora".
Bai amsa ba illa yatsine fuska da yayi cikin yanayi kamar akwai abin da ke damun sa yana mai duban yarinyar dake zaune can gefe da su ta takure waje daya a shekarun ta ba za su hau goma zuwa sha daya ba fara ce tas! kamar shuwa bata da jiki sosai kallo daya zakayi mata ka gane irin matan nan ne ma su tsayi da kirar jiki.
Duban ta sosai Alhaji Mati yayi zuciyarsa na wani irin zullon farin ciki KUDIRI da burinsa gaf! suke da cika komai na duniyarsa ya kusan zamar masa sabo filin a leda.
Takardun da yaji Uban Marayu ya turo masa gabansa ne ya tsinke masa tunanin da yake yi cikin yanayi na son abin da aka turo masa ya dauki takardun yana yawatawa da idanuwansa kan su yana mai sakin wani Shu'umin murmushi.
Takardu ne na yarjejiniyar da sukayi a tsakaninsu zuwan sa na farko da suka je kotu komai da komai gashi nan a rubuce har da sanya hannun lauya da shi uban marayun.
Duban sa yayi kafun ya numfasa.
"Uban marayu na ga komai kuma hakan yayi daidai sosai da sosai"
ya fadi yana mai dauko Biro yana sanya hannu a wajan da Uban Marayun ya nuna masa da hannunsa.
"Godiya muke sosai Uban Marayu".
Alhaji Mati ya sake fadi yaka mai mika masa hannu suna gaisawa duk kan su da murmushi a saman fuskarsu.
Matar da take gefen sa zaune ya duba yana murmushi.
"Hajiya kiyi masa godiya ta tabbata yau dai mun samu 'ya".
Tsukankiyar matar mai kama da muciya da zani fuskar nan ta ta tasha mai sai kyalli take da wani kala-kala kallo daya zakayi mata ka kau da kan ka.
Yak'e ta saki tana mai washe hakoranta da suka gama dafewa da dattin hayakin sigari godiya tayi kamar bata so ba kafun ta mike tana sabar jakarta.
 Dama tuntuni sunyi komai da komai jira kawai suke su samu damar tafiya daga wajan Uban Marayu.
"Khairiyya shikenan kuma kin bar mu kin ga yanzu ga iyayenki nan da za ki koma wajan su da zama ina yi miki fatan alheri a rayuwa".
Khairiyya dake kwakumi da jikinta da sauri ta dago idanunta da suka ci taf! da hawaye tana dubansa sosai yaji ta bashi tausayi a ransa kau da kai yayi don ya san tabbas in ya cigaba da kallon ta shima hawaye zai yi gaban sa yake ji yana bugawa amma bai kawo komai a kai ba kawai tunanin sa kamar yarda ya saba rabuwa da marayu cikin damuwa yau ma haka ne yake ji dalilin rabuwa da Khairiyya.
Kuka sosai take yi har suka fito daga cikin gidan bayan sun yi BANKWANA da yan uwanta sai kuka suke yi suma tana ji tana ga aka sakata cikin motar Alhaji Mati cikin yan mintina kalilan suka bar harabar gidan kallon gidan take yi tana ji a ranta ba za ta sake dawowa ba kallon gidan take yi kallo na karshe a filin rayuwarta tana ji a ranta bazata sake zuwa cikin gidan nan ba in ba wani iko na Allah ba sosai take ji gabanta na faduwa duk lokacin da ta kalli Alhaji Mati ko kuma taji amon muryarsa mai razana ta.
Tafiya mai nisa sukayi tun tana hango gidaje har suka fara shiga dazuka masu bishiyoyi kala daban-daban izuwa nan lokaci ta tsaigaita da kukan da take sai jan numfashi take tana ajiyar zuciya.
Awanni Hudu sukayi a hanya kafun su iso cikin Garin Sulaje suna kokarin shiga cikin gari Alhaji Mati yayi parking gefen titi yana duban matar dake gefensa zaune murmushi yake saki mai dauke da mugunta a ciki.
"kin gama aikin ki don haka ga tukuicin ki".
Ya fadi yana sanya hannu cikin aljihunsa yana zaro bandir din yan dubu dubu guda biyu ansa tayi tana mai kau da fuska kamar bata so ba.
"Sannan kuma wannan lamarin ya kasance tsakanina da ke in har naji labari mai kama da shigen wannan lamarin kin san Allah sai kin bar filin duniyar nan".
Ya karashe fuskarsa a daure kamar bakin hadarin dake kokarin zubda ruwa.
Ko a jikin ta bata nuna damuwa da maganganunsa ba illa tsaki da tayi can kasar makoshi ta na balle murfin motar ta fice Khairiyya dake takure bayan mota ta duba da wani irin yanayi na tausayawa tana faman gyaÉ—a kai kafun ta dubi Alhaji Mati.
"batar da sunanka sananne ka aro na banza ka sakawa kan ka akan wani KUDIRI naka na daban...Uhmm ba na ganin wanda ya isa rikakken mutum mara tsoro zai fito da wannan salon na boye sunan sa domin duk wanda yake so ya fado DUNIYAR SHAHARA a wani fanni da sunan sa ya kamata a san shi ko an rufe babin sa ba za taba mantawa dashi ba da abin da ya aikata".
Tana gama fadin haka ta buga murfin motar da karfi yan yatsunta biyu ta dagawa Khairiyya wacce a wannan lokacin ta dago da kanta tana dubansu su duka biyun cikin yanayin na rashin inda suka dosa a tsakanin su.
"Hajiya Layla"
Ya fadi da murmushin mugunta a laɓɓansa kafun ya dora.
"...abu daya zai sa na kyale ki a filin duniyar nan shi ne wannan yarinyar da kika bada takomashin taimako har na same ta saboda ita ce hanyar samun arzikina da nake burin cimma wa wannan dalilin zai hanani yi miki komai amma duk da haka ki tsumaye ni ina nan tafe".
yatsine fuska tayi kafun ta juya ta fara takawa kan kafafuwanta.
Dariya yake yi sosai da sosai har yana buga sitiyarin motar kafun ya tsagaita kamar daukewar ruwan sama fuskar nan tashi ya haÉ—e ta waje daya kafun yayi wa motar ki ya fizge ta kamar mai kokarin tashi sama.
 tafiya yayi mai dan tsayi mai makon ya shiga gari kawai sai ya ratse ya yanki daji hakan da Khairiyya ta gani ya dan tsoro ta ta ware idanu tayi tana duban hanyar da suke shiga daji sosai da sosai tun suna hango gidaje har suka daina sai bishiyoyi kala kala can nesa kadan ta hango wani gida shi kadai kwallin kwal! a tsakar daji ba ka jin kukan komai sai na tsintsaye da sauran halittun daji gida dan madaidaici ne anyi masa farin fenti gabadayansa haka kwanon rufin ma fari ne aka saka. A hankali Alhaji Mati ya isa kofar gidan yayi Parking ita dai Khairiyya gabanta sai faduwa yake yi ta saki baki tana kallon gidan tana jin sa lokacin da ya buÉ—e kofar ya fita kafun taji amon muryarsa akanta a dan razane ta dube shi kafun tayi kasa da kai gabanta na tsanan ta faduwa a hankali ta fara kokarin fito bayan ya bude mata kofa ya turke a gefe gyara zaman babbar rigarsa yake yi kamar wani sabon ango gefen sa ta ratsa ta tsaya hannunta harÉ—e waje guda a kirjinta.
"Muje ko".
Ya fadi yana kamo hannunta wani irin razana tayi idanuwanta sukayo waje gabadaya jikinta ya shiga rawa kamar wacce wayar wuta ta kama.
Bai damu da yanayin da ya ga ta shiga ba haka ya ja ta har zuwa kofar gidan ba tare da wani shamaki ba ya turo kofar ya shiga ba kowa a tsakar gidan sai fili kawai da aka malale da sumunti kallo daya zakayi wa gidan ka gane ya na samun gyara sosai da sosai duk girma gidan da fadinsa daki daya ne jal! sai can gefe kuma wani dan karamin daki ne wanda kallo daya zakayi masa ka gane makewayi ne.
"Dr.Erena da kan sa".
Kamar daga sama suka ji muryar ta amsa amo a filin gidan baki daya da sauri Khairiyya ta shiga dube dube don ganin daga in da muryar take amma bata ga kowa ba tana cikin wannan halin taji Alhaji Mati ya ja hannunta sun nufi dakin nan guda daya ta so ta tirje amma sai ya sa mata karfi ya shigar da ita dakin zaune su ka tadda shi babban mutum ne wanda a kalla zai baiwa shekaru hamsin baya sanye yake da riga da malum-malum farare tas sai rawa ni shima na farin kyalle ne duk dakin haka aka kawata shi da farin abubuwa dangin su kwarya da su casbaha da sauran su gabansa kuma in da yake zaune wani faskeken faranti ne shima fari ne an cika shi da yashi mai laushi sosai gefe da gefen faranti din goran duba ne cike da wani farin ruwa mai daukar ido sosai da sosai.
"Ita ce wannan?".
Mutumin ya fadi yana mai kallon Khairiyya da wata irin siga kafun ya sake duban Alhaji Mati da shima yake ta faman yashe baki burin sa ya kusan cika wannan karon Malamin sa ko mu ce boka bai katse masa hanzari ba.
"Irin wadannan ake so masu kyau da tsari sosai wanda kai a karan kanka sai kaji komai daidai amma da kaje kana kwaso yaku bayi ina aiki zai yiwu kasan komai yan son MAI ƘYAU domin har kace za ayi ta arziki da kyau kuma".
Shi dai Alhaji Mati sai zabga murmushi yake yi kamar ango a daren farko hankalin sa gabadaya ya koma kan Khairiyya da jikin ta ya fara rawa jin kalaman da suke fadi akan ta ko ba a fadi mata ba tabbas akwai abin da ake kokarin yi akanta.
Wani Alkalami ya dauko wanda aka shafe jikinsa gabadaya da farin wani abu amma daga kansa in da aka yi don dangwalo tawada bakinkirin ne sosai.
Nuna Khairiyya ya shiga yi da shi kafun ya dubi Alhaji Mati yana mai saka laɓɓansa duka cikin bakinsa yana tsotsawa kamar wanda ya samu alawa.
"Zan yi mata wani aiki yanzu ina bukatar kadaicewa ni da ita".
Ya fadi da wani murmushi a fuskarsa sosai Alhaji Mati ya shiga gyaÉ—a kai yana faman sakin yak'e haka da Malamin ya gani ya sanya shi mikewa da wani zabgegen carbi a hannunsa yana mai yawatawa akan Khairiyya kafun lokaci guda ya watsa shi gaban Alhaji Mati.
"Zabi guda daya".
Ba musu ya kai hannunsa ya sauke kan 'ya'yan carbin ya zabi daya gami da mikawa Malamin ya ansa kafun yayi jim na dan lokaci bakinsa na motsawa sannan ya tofe a jikin zabin Alhaji Mati yan sakanni ya dauka kafun ya dubi Alhaji Mati.
"Tun yanzu duniyar nasarorinka sun fara shan sharafin su don haka ka fara lissafin kan ka a cikin manya-manyan ATTAJIRAN DUNIYA".
Wani irin murmushi ya kufce masa kafun ya dubi Khairiyya yana jin wani irin nishaɗi da farinciki na ƙaruwa a ko wani fili na zuciyarsa dama duniyarsa baki daya.
"Dakyau Malam Dan-Tani".
GyaÉ—a masa kai yayi yana masa nuni da ido da yayi wa Khairiyya magana ta biyo shi ba musu Alhaji Mati ya dubi Khairiyya da ta gama hargitsewa gabadaya.
"Tashi ki bi Malam yayi maganin ganin iyayenki".
Wani irin ware idanu tayi tana dubansa kamar ta ga bakuwar fuska a filin duniyarta cikin hanzari ta mike har tana kokarin faduwa hanyar da taga Malam ya nufa nan tabi labulan da ke jikin bango taga ya yaye sai ga wata kofa ta bayyana ba tsoro komi ta bishi bayansa ta shiga.
Daki ne dan madaidai ci ba komai a cikin sai buzu babban dake shimfiÉ—e a tsakar dakin sai wata babbar kwarya wacce aka zane da rubutun sunayen Allah da farin abu shi ba fetti ba sannan shi ba tawada ba.
"Cire kayan jikin ki duka".
Kamar daga sama taji ya fadi haka a dan razane ta dawo daga tunanin da ta fada ta shiga dubansa da idanuwanta da sukayo warwaje kamar mai son fashe da kuka.
"Ki cire kayan ki nace".
Ya sake fadi a wannan karo wata murya ce mai sauti yayi maganar da ita hakan ya tsora ta ta sosai da sauri tayi baya tana kokarin ficewa daga dakin kafun ta yi taku biyu ya fizgo ta wata kara ta saki hakan da ya gani da sauri ya janyo wani dan karamin buzu ya yafa mata a fuska gabadaya jikin ta ya saki lokaci guda ta zube kasa kamar matacciya.
Cikin hanzari ya dauko wani katon Alkalami ya tsoma cikin katuwar kwaryar nan dake girke tsakar dakin bayan ya fito dashi ya shiga yan tofe-tofe din sa fuskar Khairiyya ya dosa yana wani irin rubutu a jiki shi ba chainanci ba shi ba indiyanci ba sannan shi dai gashi gashi nan za dai a iya dangantashi da na Arabic bisa wasu harufa da suke yawo cikin rubutun da yake mata a fuska.
Sai da ya zane ko ina ns fuskarts kafun ya zare dan kwalin dake kanta sosai gashin kanta ya bazu wanda ya kasance mai yawa gashi baki sidik!
Sannan ya zare rigar jikinta nan ma zane mata jiki yayi da rubutun kafun ya zare mata dogon wandon dake jikinta da dan kanfai dinta nan ma zane ta yashiga yi ta ko ina har da farjinta..
(Wa'iyazubilla!)
sai da ya tabbatar ko ina na jikinta ya samu rubutun da yake yi kafun ya dawon kan gashin ta ya shiga ya mutsawa da ruwan da yayi rubutun sannan ya mai da mata da kayan jikinta sakanni kadan da kammalawar ya dauko buzun nan ya shafa a fuskarta lokaci guda ta dawo hayyacinta da sauri ta mike tana kokarin zurawa da gudu ya sanya hannu ya kamota ya zaunar da ita.
"Ba abin da zan miki zauna ki huta yanzu za ku tafi ki ga iyayenki".
Ba musu ta koma ta zauna shi kuma ya tashi ya fice wajan Alhaji Mati ya koma kafun ya zauna yana mai jan carbin da ya samu zube.
"An kammala komai yanzu aiki ya rage gareka".
GyaÉ—a kai yayi yana faman murmushi kafun Malamin ya cigaba da cewa.
"Aikin da yake gaban ka yanzu shi tun daga daren yau za ka fara amfani da ita wato saduwa har na tsawon kwana uku a ko wani kwana daya kuma sau uku zaka sadu da ita a dare ka ga ya kama sau tara kenan zaka sadu da ita a dare uku daga ranar da ka cika kwana ukun to a ranar zata bar gidan ka karka sake ko minti tara ta kara domin za a iya samun matsala mai girma wanda za ta iya ruguzo aikin mu da muka É—ade muna kokarin cimma sa".
Wani irin dokawa gaban Alhaji Mati yayi amma bai bari Malamin ya gane ba ya shiga yaƙe yana sharce gumin da yake ta faman tsantsafo masa duban Malam yayi.
"Amma Malam kai fa kace ba zan taba kusantar mace ba Amma kima yanzu...".
"Nasan da haka shiyasa nace daga dare na uku karka sake kulata kar ma ka sake ta kwana gidan ka".
Hadiye miyau yayi mai tauri jin samun mafita da yayi amma da duk ya gama ruÉ—ewa jin bayanin da Malam din yayi masa.
"za ku iya tafiya".
Ya fadi ya na kau da kai daga kallon sa.
Tashi Alhaji Mati yayi jiki a sanyaye ya kira yi Khiariyya da sauri ta fito tana duban su daya bayan daya.
"Zaka ji sako na Malam Dan-Tani nan zuwa gobe".
Bai ansa masa ba illa gyaÉ—a kai da yayi.
Hannunta ya ja suka fice bayan yayi masa Sallama.
Suna shiga mota ya dau hanya izuwa lokacin dare ya fara shigowa sosai don har an idar da Sallar issha'i.
Cikin mintinan da ba su haura talatin ba suka isa wani tankameman gida mai rai da lafiya wanda kallo daya zakayi masa sai kayi zaton ba a filin kasar najeriya yake ba saboda yanayin tsarin gininsa da kayan alatun da aka zuba.
Bayan yayi Parking wajan sauran motocin gidan suka fito yana rike da hannun Khairiyya har suka isa kofar da zata sada su da baban falon gidan key ya saka ya buÉ—e suka shiga.
Yaa Allah!
Zo ku ga Aljanar duniya tsayawa tsara suffar falon ma katon aiki ne a gare ni ku dai ku baiwa kan ku amsa da kan ku makaranta.
Zaunar da iya yayi akan duma duman kujerun Falon kafun ya zare babbar rigarsa ya yasar a nan ya sake cire yar ciki ya sake ajjewa ya shiga kokarin kwance wandon sa da sauri Khairiyya tayi kasa da kai tana dukunkunewa waje daya numfashinta taji yana sama da kasa kamar zai dauke sosai da sosai ta firgita zuciyar tashiga bugu ba ƙaƙƙautawa.
Ba ta san lokacin da ya iso gareta har ya zauna ba kawai jin hannun mutum tayi a jikinta da sauri ta kara takurewa kafun ta dago idanuwanta da suka rine lokaci guda.
'Innalillahi wa inna ilair raji'un'.
Abin da ta fadi kenan a zuciyarta ganinsa tumbur haihuwar uwarsa komai na halittarsa a bayyane yake ba ta san lokacin da ta saki wata wawuyar kara ba gami da kokarin mikewa amma ina ta kasa domin lokaci guda taji ya daukota gabadayanta ya ajje kan cinyarsa ya shiga yage duk wata suntura dake jikinta fuskarsa dauke da murmushin mugunta wani irin yanayi yake ji a jikinta dama zuciyarsa baki daya ya shiga lumshe idanuwansa bayan ya kammala zare mata komai na jikin ta ta koma haihuwar uwarta ita ma kuka take yi wanda bata san lokacin da ya kufce mata ba sai faman tirje tirje take amma ina hakan bai hanashi haike mata ba cikin yanayi na karfi yake sarrafata kamar zai karyata ita kuwa ihu take yi amma ina ba alamun wani mai cetonta tun tana ihun har muryar ta ta dashe lokacin da ya shigeta tun da ta saki wata kara bata sake sanin in da kanta yake ba har yayi kidin sa yayi rawarsa ya ta shi ya barta nan yashe cikin yanayi na tashin hankali da taba zuciya komai nata in ka kalla sai ka kau da kai domin kace kace yayi mata kamar ba mutum mai rai a jiki ba kujerar da take kai kuwa kamar an yanka kaza a wajan tayi FESHIN JINI haka ya koma.
Ba ita ta farka ba sai cikin dare sosai da wata irin kara ta saki ta tashi jikinta na kyarma kuka take yi kuka mai taba zuciya kuka ne take yi wanda ba ta san iya lokacin da zata daina shi ba ko ina na jikinta ciwo yake yi mata ga wani zafi da raÉ—aÉ—i da take jin sa ya na amsa wa har cikin kanta tun daga mararta har zuwa kafafuwanta ji take yi kamar ana saka guduma ana kwankwatsa su.
Cikin wannan yanayin garin Allah ya waye haka ya fito ya tadda ita ko kallon arzuki bai yi mata ba ya sa kai ya fice bai sake dawowa ba sai dare a wannan daren ma haka ce ta kasance don Khairiyya ji tayi kamar a daren ranar da ya kawota gidan ba komai yayi mata ba don sai da ta gwanma ce da ma ta mutu suma dai bata san iya adadin da tayi ba.
A dare na uku kuwa har yayi ya gama bata ta sani ba don gabadaya ba numfashi a jikinta shi kansa sai da yayi tunanin mutuwa tayi yana kammala abin da yake yi ya mai da kayansa ya dauke ta a cikin wannan mugun halin ya saka ta a motarshi yaja ya fice daga cikin layin sosai yayi nisa da unguwarsu kafin ya sami gefen titi ya fito a hankali kamar wanda fitsari ya matsawa zai yi haka ya ja motar sosai gefe yayi Parking ya fito ya buÉ—e ya zaro ta har zuwa lokacin ba numfashi a jikinta ya yasar da ita sai da ya dubi gabas da yamma kudu da arewa ya ga ba wanda ya gan shi domin lokacin dare yayi sosai da sosai ya ja motarsa yayi gaba zuciyarsa fes! KUDIRI da burinsa sun cika zai zama daya daga cikin ATTAJIRAN DUNIYA.
Gudu yake yi sosai fuskarsa na bayyanar da jin dadi har ya koma gida yayi wanka ya shige dakin sa ya baje saman kafcecen gadonsa yana faman sakin numfashi na farinciki da jindadi har barci barawo yayi awan gaba dashi.
*****
 sosai take jin gabanta na faduwa tun daga nesa idanuwanta take kara warewa sosai daga cikin motarta har ta iso wajan tayi parking gabanta na tsananta faduwa.
'Innalillahi wa inna ilaihir raji'un'.
Ta fadi tana mai daura hannu akai tana mai rushe da wani irin kuka.
"Khairiyya".
Ta kira sunanta da wata irin muryar mai cike da tashin hankali da tsananin kaÉ—uwa isa tayi gareta tana janyota daga cikin ciyayin da take rintse idanuwanta tayi lokacin da ta ga mugun halin da take ciki.
"Na shiga uku ni Layla wani irin mugun abu nake shirin gani a filin duniyar rayuwa ta ne".
A daidai lokacin hannun Khairiyya yayi motsi ganin haka ya sanya ta jijjigata amma ina ba alamun zata iya ko da sake motsi a halin da take sai dai numfashin da ke fita daga hancin ta cikin yanayi na tsananin wahala da yanke rayuwar duniyar nan.
Kuka sosai Hajiya Layla ke yi tana faman kiran sunan Khairiyya amma ina ba alamun motsawa da sauri ta sungume tayi motar ta da ita cikin tsananin tashin hankali har zuwa lokacin hawaye ba su daina zuba a idanuwanta ba zuciyarta na faman karyewa da wani irin yanayi mai girma na tashin hankali.
"Alhaji Mati-Dr.Erena".
Ta fadi cikin yanayi na takaicin zuciya da ruhi sosai ta zauna kan set din motar tana hada kanta da Sitiyari wani numfashi take saki a wahale mai tsananin zafi da ku na.
"Ban san rashin imanin naka ya kai haka ba, ban san baka da tausayi har haka ba, ban san abin da yasa na yarda har na san ka a rayuwata ba, ban san mai yasa na anshi bukatarka ba, in da nasan kudirin da ke ranka kenan ba zan taba yarda har hakan ta faru ba".
Numfashi taja kafun ta cigaba cikin muryar kuka.
"na tsani kaina na tsani rayuwarta da nayi da kai a duniyata Alhaji Mati ban san har lamarin naka ya kai haka ba ban san da wani ido zan kalli yarinyar da na saka hannu wajen KETA HADDI a gareta ba ban san wata irin tsana za tayi mani ba in har tana da sauran rayuwa a duniyar nan kaico na kaicon wannan rayuwa kaicon haduwa da irin ku Alhaji Mati a wannan duniyar na tsane ka na tsane duk mai hali irin naka na tsani sake ko da ganin fuskar ka ce a wannan rayuwa".
Hannu ta sa ta dauke zafafan hawayen da take jin su kamar za su dauke mata fatar fuska kafun fuskarta ts kara tamkewa kamar Alhaji Mati na gabanta.
"ka tsuwa maye ni Alhaji Mati na rantse maka da Allah sai ka ga ne kurin ka sai na mai da Khairiyya mace sai na mai da ita mai 'yanci sannan kuma da hannunta za ta dauki fansa ka jira lokacin ka Alhaji Mati yana nan tafe".
Ta karashe idanuwanta na zubda hawaye kafun ta saki wani murmushi mai ciwo a zuciya da ruhi.
Juyawa tayi ta dubi Khairiyya wani kuka ne ya zo mata da sauri ta dake kafun ta fizgi motar ta cilla saman titi gudu take yi kamar zata tashi sama...
*******
A hankali ta dago fuskarta tana kallon Get din da zai kaita cikin ABDURRAZAQ FASHION CLUB COMPANY.
ba za ta iya shiga ba da yanayin da take ciki a fuskarta ba zata iya zuwa ta kalle shi ba ba ta san mai za tayi masa ba a daidai wannan lokacin in har suka hadu a waje daya.
Da sauri tayi wa Motar Key cikin wani irin yanayi na tashin hankali amma fuskarta wani murmushi yake bayyana a kanta juyar da akalar motar tayi ta cilla saman titi kamar zata tashi sama haka take zabga gudu.
*KAMALA MINNA*😘😘
Post a Comment (0)