TAIMAKON MABUƘACI YA FI KA KOMA HWJJI BAYAN ZUWAN FARKO


TAIMAKON MABUKACI YA FI KA KOMA AIKIN HAJJI BAYAN ZUWANKA NA FARKO!


_Mutum ya bayar da dukiyarsa ga wanda bashi ya tauye masa don ya biya bashin, ko ya bayar da ita ga Matalauci, ko wanda iyalai suka yi masa nauyi don ya kula da iyalinsa, ko ya ba mai rainon maraya don ya yaye masa wahala, ya fi alkhairi fiye da mutum ya tafi aikin Hajji sau dari bayan zuwansa na farko._

_Domin hakika cusa farin ciki cikin Zuciyar musulmi da taimakon wanda ke cikin kunci da yaye wahalar Mabukaci da taimakon mara karfi ya fi Hajji dubu bayan na farilla._

_Allah Ya bamu ikon taimakawa mabukata._

_*✍🏿Ayyoub Mouser Giwa.*_

_Daga Zauren_
_*🕌Islamic Post WhatsApp.*_

_Domin kasancewa tare da mu a group din *Islamic Post WhatsApp* sai a turo da cikakken suna da address zuwa wannan number *08166650256.*_

Wassalamu alaikum Warahmatullahi Wabarakatuh.
Post a Comment (0)