KUSKURENA YA YIN DA NAKE SALLAH 07


*KUSKURENA YA YIN DA NAKE*
                *SALLAH*

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

*FUTOWA TA 👇*
            *(7)*


*FUTA DAGA MASALLACI BAYAN GAMA KIRAN SALLAH BA TARE DA WANI UZURI BA*

    Abun da ya tabbata acikin sunnar farin jakada babban dan Abdullah Muhammadurrasulullah saw ga duk mutumin da ya shiga masallaci ladan ya kira sallah kada ya futa sai idan da bukata, dalili akan haka hadisin Abi Huraira yake cewa manzan Allah saw ya umarcemu Yake cewa:IDAN KUKA KASANCE ACIKIN MASALLACI AKA KIRA SALLAH KADA DAYANKU YA FUTA HAR SAI YA YI SALLAH ". 
   shi yasa Abu Huraira kamar yadda Abi sha'asa ya rawaito yaga wani an kira sallah sai ya tashi ya futa daga masallaci sai yace hakika wannan ya sabawa Baban Qasim. 
   Malami sun tafi akan haramcin futa daga masallaci bayan kiran sallah ba tare da wani uzuri ba kamar alwala ko biyan bukata ko kuma abun da babu makawa ga mutum sai ya futa, me yuwuwa illar da ta saka hakan shine saboda kaucewa Mummunan zato tsakanin musulmai, ya yin da yaga mutum ya futa daga masallaci bayan kiran sallah ba tare da wani uzuri Mummunan zato zai iya shiga tsakaninsa da "yan uwansa musulmai.


*ALLAH SHINE MASANI*

🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌🕌

*MU HADU A FUTOWA TA (08)*

*Rubutawa... ✍️✍️✍️✍️✍️*
             *Dalibi mai neman ilimi Nazifi Yakubu Abubakar*
          *(Abu Rumaisa)*
        🥏08145437040🥏
Post a Comment (0)