MENENE AKA HANA WANDA YAKE SAN YIN LAYYA YA AIKATA?

MENENE AKA HANA WANDA YAKE SAN YIN LAYYA YA AIKATA?

الحمد لله، سبحانك اللهم لا علم لنا إلا ما علمتنا إنك أنت العليم الحكيم.

AMSA:

Idan Watan zul-hijjah ya kama, haramunne akan Namiji ko mace da ya kesan yin layya, ya yanke farcensa ko sumarsa.

Saboda hadisin da Muslim ya ruwaito (1977) daka Ummu Salama Allah yaqara mata yarda daka Annabi Sallallahu Alaihi wasallam yace: ( Idan Kuka ga Watan zul-hijja, kuma dayanku yana san Yin layya, ya kame  daka yanke farcensa ko Aske gashinsa)

Imamun Nawawi Rahimahullahu yace: Malamai Sunyi Sabani akan wanda watan zul-hijjah ya kama yana san yin layya.

Sa'eed da Ibnu Musayyib da Rabi'ah da Ahmad da Ishaq da Dauda da Wasu MalamanvSahafi'iyyah sukace: Haramunne mutum yacire komai na gashinsa, da farcensa, harsai yayi layya, shafi'i yace: Makaruhine karhanci na Kamala, ba Haramun bane.

Sharhin Muslim.

Mace ya Halatta ta Tsefe gashin kanta, ta Wankeshi, Saidai kada ta Tajeshi, Abunda ya zuba na gashinta yayin tsefewa da Wankewa Baya cutarwa akan layyarta.

Fatawa bin Baaz (18/47).

Ya Halatta Wanda yake da Niyyar layya ya gyara tufafinsa ko yasa turare ko yin jima'i.

Wallahu A'alamu.

سبحانك اللهم وبحمدك أشهد أن لا إله إلا أنت، أستغفرك وأتوب إليك.

Tambaya da Amsa Abisa fahimtar Magabata Na Kwarai

WhatsApp Group

2348123432272

Post a Comment (0)