WADANNE ABUBUWA NE IDAN SUKA BI TA GABAN MAI SALLAH SALLAR SA TA BACI?

*Asssalamu Alaikum* . . *Tambaya ta 3,238:* = Wadanne abubuwane idan sukabi ta gaban me sallah, sallarshi tabaci. = = Amsa = _Sune; Mace balagaggiya, jaki, sekuma baqin kare. Wadannan sune ababe guda uku wadanda Annabi (s.a.w) yace idan suka wuce tagaban me sallah sun bata masa sallah. Duk da cewa a wata ruwaya Aisha tace karyane batayardaba cewa Annabi yace har mace idan tawuce sallar ta 6aci kuma takafa hujja cewa tana kwanciya agaban Annabi alhalin yana sallah****_ _Amma wannan maganar ta Aisha malamai basu kar6etaba saboda shi hadisin akan wucewa yayi magana bawai akan zama ko kwanciyaba. Sannan kuma tunda hadisin Annabi ya tabbata wayake zance Su Aisha kuma?? Wannan bayanin kana iya duba Fathu zuljalali wal Ikram, wato sharhin bulugul maram na Ibnu Usaimin ya tattauna matsalar dakyau a karkashin wannan hadisin********_ = = Allah Yasa mudace . . *DAGA ZAUREN* . *KITABU WAS SUNNAH* . *مجلس تعليم الكتاب والسنة* 📓📔 Watsaps 08036222795 09031200070 . . Zaku iya samun shafinmu na facebook ta wannan hanyar http://m.facebook.com/Kitabu-Wassunah-1522000298067561/ . ﺳﺒﺤﺎﻧﻚ ﺍﻟﻠﻬﻢ ﻭﺑﺤﻤﺪﻙ, ﺃﺷﻬﺪ ﺃﻥ ﻻ ﺇﻟﻪ ﺇﻻ ﺃﻧﺖ، ﺃﺳﺘﻐﻔﺮﻙ ﻭﺃﺗﻮﺏ ﺇﻟﻴﻚ. . Subhanak Allahumma wabi hamdika ash hadu anla ila ha illah anta astagfiruka wa atubu ilaika
Post a Comment (0)