Mairo 56

 *♡... MAIRO ...♡*

*BY*

     *_KHADEEJA CANDY_*
Candynovel.wordpress.com

Vote me on Wattpad @Khadeeja_Candy

_GODIYA NAKE SANAH S MATAZU UMMU BEENAH_πŸ‘πŸΏ

*65*

        *_K'ARSHE_*

Taimakon gaggawa likitocin suka shiga bashi cikin taimakon Allah numfashin nashi ya dawo dai-dai,
   Su Momi na tsaye waje cirko-cirko likitocin suka fito. Jiki na rawa Momi ta shiga tambayar Ι—ayan likitan “Yana da rai kuwa?"
  Sai da ya sauke ajiyar zuciya sannan yace “Yana da rai amman abinda kukayi kasada ne babban dan ba'a nunawa marar lafiya abinda zai tada mishi hankali irin haka"
   "Alhamdulillahi" Mansura ce tayi godiyar tana share hawaye, Doc yace “Daga yanzu kada wadda ya sake shiga Ι—akin sai da izinin Dr"
Kai Momi ta gyaΙ—a dai-dai lokacin Siraj ya iso yana faΙ—in “Ance numfashinshi ya Ι—auke?"
   “Eh amman ya dawo yanzu komai na tafiya dai-dai" Dr ne ya bashi amsa
   
Kanshi ya shafa yayi ma Allah godiya Dr ya kalleshi yace “Dr Siraj kayi mishi tiyatar yanzu kaiwa dan akwai jijiyar da take taushe mashi numfashi kaga idan akayi komai zai zama dai-dai"
   Siraj ya nisa yace “Nima haka nake tunani dan idan ace sai ya warke za'ayi toh kamar wani sabon ciyon ne kuma"
   “Good haka nake nufi kuma kaga idan zai warke zai warke gaba Ι—aya ne ba sai yayi jinya biu ba"
   “Haka za'ayi amman sai naga tafiyar numfashinshi tukuna sai naga yadda abin yayi"
    “Okey haka yayi amman karka sake bari wani ya shiga Ι—akin koda Momi ce" Ya faΙ—a yana murmushi.
     Kai Siraj ya kaΙ—a mishi yana kallon Momi sannan ya nufi Ι—akin,

Saida Siraj ya Ι—auki awa biu yana ganin tafiyar numfashinshi sannan yasa aka shirya mishi komai ya shiga Ι—akin tiyata dashi,
   
Awarshi hudu Ι—akin tiyarta har da yan muntuna sannan ya fito tare da wasu manyan likitoci, saida ya shiga wani Ι—akin ya cire kayan daya fito dasu daga Ι—akin tiyatar sannan ya nufo gurin su Momi.
     A fuskarashi Momi ta karanci abinda ke bakinshi, da murmushi ya k'arasa yana kallon Momi da ita murmushin take idonta da hawaye.
   “Anyi nasara Momi babu sauran kuka sai dai ayi adduu Allah ya bashi sauki"
  Godema Allah Momi ta dinga ita da Mansura da sauran yan uwa da suke gurin,
  Murmushi Siraj yayi ya nufi k'ofar Ι—akin da aka chanja ma Qasin, a nan ya tararda Yarima tsaye hannayenshi sanye cikin aljihu,
          Uffan Siraj bai ce mishi ba sai ma kauda kai da kuma yayi, murmusawa Yarima yayi ya mik'a mishi hannu yana faΙ—in “Congratulations Siraj"
Hannun nashi Siraj ya kalla sannan ya kalleshi “Banyi zato wannan daga gareka ba so tell me minene sirrin?"
    Murmushi Yarima ya sakeyi yace “Babu komai Siraj kuma bana so ka sake daukata cikin makiyan Qasin no more"
    Fuskarshi Siraj ya k'urawa ido nan Yarima ya k'araso kusa dashi ya dafashi “Siraj abinda ya samu Qasin ya karantar dani abubuwa da yawa just look at him da ace mutuwa yayi da yayi kyakkyawar cikawa kowa yana kuka da rashin shi ni kaina ban taba jiya n abinda naji game Qasin ba irin wadda na daga jiya zuwa yau,
  Siraj Qasin yana da farin jini gurin kowa ba kuma komai ya jawo mishi wannan ba face kyakkyawar mu'amala da kowa"
   Sukuku Siraj yayi yana kallonshi kamin yace “Yarima kaine da kanka kake wannan maganar?"
   “Nine Siraj ina nadamar abinda nayi ma Qasin da ace ya mutu da bansa ya duniya da mutane zasu kalleni ba bansan abinda zan fadawa ubangijina ba"
    Ajiyar zuciya Siraj ya sauke yace “Idan har da gaske kayi nadama ba afurincika kawai za'a gani ba a aikace za'a gani Yarima zanfi kowa jindaΙ—i idan ka zubarda duk wani mummunan hali nake ka chanja rayuwarka ka maida kanka ba kowa ba,
  Mulki fa ba ya dawwama kamar yadda sarauta bata dawwwama dole ne ka barsu ko su barka shin idan da tunani mutuwa miya zau kawo girman kai da Ι—agawa baka fi kowa ba a gurin Allah kuma babu wadda ya fika sai wadda yafi wani tsoron Allah,
idan har da gaske ne toh zanfi kowa farin ciki da haka"
   Yarima yace “Inason ka zubarda duk wani kallo da kake mi na marar kyau hali ko kuma wadda zai iya cutar da kai ina son mu koma normal bida Qasin"
    Murmushi Siraj yayi “Nima zanso haka sai dai har yanzu gani nake kamar ba Yariman dana sani bane"
   Murmushi kawai yayi ya juya yasa hannun shi aljihu ya nufi kofar da zata fitar dashi daga gurin gaba Ι—aya,
Da ido Siraj ya bishi har ya fice,

Kai tsaye gida ya nufa gurin hajiya,
     Parlor ya sameta kishingiΙ—e ita da bak'inta suna fira, tana ganin shi ta zaune yana kallon shi.
  'Daya bayan Ι—aya ga bisu duk sai da ya gaishe su, sannan ya nufi cikin Ι—akin,
Ba Hajiya ba har ba har su saida sukayi mamakin abinda yau Yarima yayi musu abinda bai tanaΙ“a.
     Tashi Hajiya tayi ta tufa mishi baya zuciyarta cike da tambayoyi ta shiga Ι—akin,
Yana ganinta ya sakar mata murmushi "Hajiya ta?"
“Na'am Yusuf"
Sai ta zauna sannan tace “Ka chanja Yarima fiye da yadda nake tsammani ka fara zama yadda nake mafarkin zaka zama"
  “Yafiyarki nake nema nasan na Ι“ata miki da yawa"
   Kai ta girgiza mishi tana murmushi “So nawa kake so nace na yafe maka Yusuf? Na faΙ—a maka nida Mai Martaba tuni muka yafe maka babu sauran Ι“acin ranka cikin ranmu"
   Dukawa yayi har k'asa yace “Hajiya ina neman wata alfarma agareku?"
  “Ka faΙ—i ko minene zanyi maka shi Yarima"
  “So nake ku zaΙ“a min matar Aure keda Mai Martaba"
Wani irin daΙ—i Momi taji sai kawai idonta suka cika da kwallah.
  “Na gode Yusuf Allah yayi maka albarka zamu zaΙ“a maka matar data dace da kai In'sha Allahu"
   Tashi yayi tsaye ya rumgume ta ya lumshe ido.

     *Wannan kenan*

  ***
Ranar da Mairo ta cika sati Ι—aya da haihuwa yaro yaci suna Yusuf sunan Yarima akayi mishi lak'ani da little Yarima sosai Yarima ya jindaΙ—i karku so ganin irin kayan da yayima jariri da uwar shi,
  AΙ“angaren su Momi basai na faΙ—a muku irin kayan barka da ta zuba ita da mutanenta ba dan kusan hausawa sunce abu namu.....
  Su Gwaggo kan bana cewa komai dan nasu farin cikin baya faΙ—uwa,

   ***   ***   *** 
Ciyo ne yake zuwa nan take amman Lafiya sannu-sannu take Shiga haka Qasin ya cigaba da jinya yana samu kyakkyawar kulawa daga Ι“angaren mtanshin da kuma Momi, Yarima da Hajiya ma ba baya ba kusan kullum sai yajs Asibitin har ya samu sauki aka sallame shi,
    Ranar daya dawo gida Mansura da Mairo kamar su zuba ruwa k'asa su sha dan murnar, anan gasa ta shiga tsakaninsu kowace ta rik'a k'ok'arin ganin ta kyautata mishi kuma suka haΙ—a kansu kamar babu abinda ya taΙ“a shiga tsakanin su,
      Bayan wata hudu da sallamar Qasin daga Asibiti aka Ι—aura Auren Yarima da Amaryar da Hajiya ta zaΙ“a mishi yar wani tsohon kwannan katsina,
    An zubarda nera tsayawa faΙ—a muku irin shagulgulan da akayi a biki Ι“ata lokacine, manyan mutane suka halarci bikin ta ko ina.

***
     Bikin shi da wata biu akayi na na Siraj da Amaryar shi a Abuja akayi komai can ne Mansura ta ziyarci wata Asibiti mai zaman kanta dan a duba mata lafiyar mahaifarta.
     Duk wani bincike da ya dace saida likitocin sukayi sannan suka tabbatar mata da bazata iya Ι—aukar ciki ba dan mahaifarta ta lalace sosai ta yadda bazata iya rikon ciki ba,
Bakin ciki Mansura tayi sosai tayi dana Sanin abinda tayi.

***

Little Yarima nada shekara da wata biyar Mairo ga sake samu ciki. Murna gurin Momi da Qasin ba'a magana, Qasin kamar ya haΙ—e ta dan farin ciki.
    Cikin jindaΙ—i ta kwanciyar hankali tayi fa rainon cikinta har ya girma ta haifo yan biu duk mata, aiko lokacin ne Qasin yace bata ga komai ba indai so da kauna ne yanzu na fara nuna mata shi.
   Mairo tayi sani fari tayi bulbul gwanin shawa'awa Mansura ma ba bayab dan duk wani bacin rai nata aje shi tayi gefe suka rika juna ita da mairo kamar ba kiyashi ba ba zaka gansu kace wani abu ya taba shiga tsakanin su ba,

AΙ“angaren Yarima ma ba shida wata matsala shida matarshi farin ciki ne da jindaΙ—i kawai a gidan duk wani hali nashi marar kyau ya zubar suka koma shi da Qasin kamar AMINNAN JUNA, Momi tafi kowa farin cikin ganin halin da su Qasin da Yarima suke yanzu,
  Ita da hajiya suka koma kamar yadda suke da komai normal.
Suka shiga wata sabuwar rayuwa mai cike da jindaΙ—i.

TAMMAT BIHAMDILLAH!
Oh Allah hope for your mercy. Do not leave me for myself. Correct all of my affairs for me.
Anan na kawo karshen wannan littafin mai suna MAIRO kurakuran dake ciki Allah ka yafe min yar karamar faΙ—akarwa dake ciki Allah yasa mu anfana da ita, duk da ba a nan naso na tsayawa amman ku kuka hanani kashe Qasin 🀷🏿‍♀.
 
SPECIAL THANKS TO
Nagarta writter's Association
W. A. F Association
Tsintsiya writers Association
   And some of my co_Writer's

Love you all my fan's and readers Allah ya haΙ—a mu da alkharinsa
Amin.

*KHADIJA ABUBAKAR ALK'ALI CEπŸ‘ŒπŸΏ*

KE MUKU BISSALAM πŸ™ŒπŸΏ

Post a Comment (0)