MAIRO 01

*♡...  MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*1*

"Na rantse da Allah yau sai an biyani ni babu ruwana"
rik'e take da kunkuru tana marmaɗen ido da murguɗa baki jikinta sai rawa yake wai ita ga matsifaffeya.
yaron dake gabanta ya risina har k'asa yana bata hak'uri
"dan Allah Mairo ki yafe min wlh ba zan kara ba ni naga kinje wani gurin ne shiyasa na cika miki ban san ba kyaso ba"
sai a lokacin ta kalleshi cikin matsifa tace "saka nayi cewa nayi na cika min kai mai hegen salo yau ko saika busar dashi ko na maka hegen duka"

wata dattijuwa take wanki gefen kogin ta kalleta tace "ke Mairo wai miyasa baki jin magana ne yanzu miye laifin yaron nan dan ya cika miki tulu?"
harara ta watsa mata ta murguda mata baki "ke kuma tsohuwa ina ruwanki dake nake yi ne da zaki samun baki ko sashi nayi da zai cika min tulu wannan ai rainine"
"ke fa baki da kirki Mairo daga magan zaki wani taso min kamar wata warinki"
"mtsssss yau daman kin san ba warinki nake ba kika samin baki a magana dan neman tsokana"

daidai nan Almu ya iso da jakinsa da jalkunan ɗinba ruwa.
yana kallon Mairo yasan matsifa ce take ganin yadda take marmaɗen ido tana rawar jiki
murmushi kawai yayi ya gaida dattijuwar

"inna ina kwana?"

"lafiya kalau Almu an tashi lafiya?"

"Alhamdulillah inna"

kallon mairo yayi "ke lafiyarki kike wannan harare2?"

banza ta masa ta cigaba da karkada jiki.
inna ta taɓe baki

"ai haka take indai rashin kunya ne ta iya ga yar banzar matsifa"

juyowa mairo tayi kanta "wai ke ina ruwanki dani kinga ban hega saggarki ba ki fita tawa bana son shinshigi"

da marmaɗe2 ta ksrasa maganar tana murguda mata baki.
      mari Almu ya kai mata ya fizgota ya jefar
"ke wai miyasa rashin kunya yayi miki yawa kamar inna zaki tsaya kina faɗawa irin wannan maganar sa'arki ce?"
wani ihu mairo ta saki ta shiga murk'ususu cikin kasa tana jan gashin kanta
"wayyo na shiga uku ya kashe ni wayyo Allah ya kare ni wayyo gwaggo"

tsoro Almu yaji ganin yadda take ihu duk'awa yayi ya rikota "tashi mu gani?"
wani mugun cizo ta kai masa a hannu saida ya saki kara ya saketa da sauri.
inna ta rike baki "oh ni hajjo wannan wace irin masifaffiyar yarinya ce haka?"
Almu dai shiru yayi yana murzar hannun dan ba karamin cizo tayi masa ba,
ya dade a haka kamin ya nufi kogin ya shiga cika jalkunansa.
       ihunta ta cigaba dayi tana murje2 daga Almu har inna babu wadda ya sake bi ta kanta.
Almu na daf da cika kayansa halilu ya iso gurin yana ganin mairo yayi saurin ta data "ke lafiya miya faru?"
langaɓe masa tayi ta cigaba da kukan
nan ya kalli inna da Almu ya shiga tambayar su ba'asi "wai miya sameta ne haka?"
inna tace "babu kawai rashin kunya tayi min Almu ya ɗan zungureta shikenan fa ta faɗi ta shiga koke2"
cikin kuka Mairo ta ɗago "wlh karya suke itace ta fasa kuka tace masa na zageta shi kuma ya ɗaga ni sama ya jefar na kare"
tana kaiwa nan ta saki wata kara kamar wadda aka sokawa wuka.
rik'e baki inna tayi jin irin karyar da Mairo ta zagga
Halilu ya kalli Almu "haba Almu ya zaka mata haka kamar wata warinka ko namiji"
Almu yayi murmushi "haba dai Halilu sai kace bakasan halin Mairo ba wlh karya take"
Halilu yace  "wai minene mafarin wannan masifa?"
inna tace "ɗiban ruwa tazo fa saita eje tulun ta tafi yawonta shine haruna ya dauka ya cika mata shine data dawo tace sai ya biyata shine ya zubar da ruwan daya zuba kuma duk da haka tace wai saiya busar tulun yadda yake shine ya shiga bata hak'uri taki hak'ura wai ita saita dake sai natibmata magana shine fa ta shiga fada min magagganu har Almu saida tayi masa rashin kunyar"
Halilu yace "daman shine kawai take yiwa wannan kuka?"
"shine kawai babu wani abun da akayi mata"
cewar inna.
kai halilu ya kaɗa ya Nufi ecen dogon yaro ya k'allo ya juyo gurin mairo cikin zafin nama ya watsa mata ita,
mairo najin saukar bulala ta tashi da gudu ta nufi gida tana uhu.

***   ***   ***

da ihu ta isa gida tana murxa gurin da Halilu ya buga mata bulalar.
da sauri gwaggo ta tare ta "lafiya Mairo miya sameki?"
rumgumeta tayi "wayyo gwaggo zasu kasheni gwaggo basa sona sun min taro suna ta duka na"
gwaggo ta dagota "su waye Mairo faɗa min uban wa ya taba ki cikin garin nan?"
cikin kuka ta shiga yima gwaggo k'arya data saba "tsohuwar gidansu hajara ce tace wa Almu wai na zageta shine shi kuma ya daga ni sama ya jefar gwaggo ya k'arya ni na bani mutuwa zanyi"
da sauri gwaggo ta zaunar da ita ta shiga duba ta tana matsifa "wannan wace irin k 'etace haka wlh duk suka karyaki sai munyi shari'ah dasu mugayen mutane azzalumai"
gwaggo na taɓa mata k'afa ta saki wani mahaukacin ihu "wayyo na shiga uku gwaggo nan gurin Halilu ya buga min ecce"
gwaggo tayo waje da ido "ecce kuma yaushe mi kika masa?"
"ban masa komai ba daga zuwansa suka fada masa k'arya shine ya dauko k'aton ecce ya buga min gwaggo basu sona na shiga uku"
tashi gwaggo tayi ta shiga ɗaki ta ɗauko mayafinta ta nufi kofa.

  
        '''
NOTE'''
*_Assalamu Alaikum ina bawa fans ɗina hak'uri bisa ga rashin ganin cigaban novel ɗina mai suna LAMARIN DUNIYA na k'are novel ɗin gaba ɗaya kamin na fara posting sai phone ɗina ya samu matsala kuma wadda nayi publishing a blog ɗina blog ɗin ya samu matsa. ta dalilin matsalar da phone ɗina ya samu amman ana kan gyara blog ɗin da zarar an kare zanyi muku C & P Insha Allah ko kuma na baku blog address ku karanta bayan haka dan Allah ina rokon duk mai novels ɗina ko wane iri ya turo min ta wannan number_*
+2348036126660
*_taku har kullum Khadeeja Candy_*

© *Khadeeja Candy*

Post a Comment (0)