TUN KAFIN AURE 38

TUN KAFIN AURE💐38




Rosie tace dadina dake ba kya cin ribar abu. Kin fiye rashin hakuri kamar gudawa. Ki zuba ido yau a jikinki zai angwance. Ki dai sha kaya da kyau don ki kara kama shi a hannu.

Hamida ana ta rawar kafa kamar ita ce zata tare. Nasihohi da adduoi Hajiya da mummy suka yi wa Hafsi. Hamida taja hannunta masu aiki suka bi bayansu da akwatunanta. A ciki suka tarar da Nafisa da yaranta 'yan mata biyu Ummu mai sunan mummy da Husna. Suna ganin Hafsi suka kankameta suna murna. Nafisa tayi musu tsawa ku sake ta mana haka kada ku kayar da ita. Husna yar shekara biyar tace Mama Hafsa ni a nan zan zauna tare da ke ko. Hamida tace asheUncle Junaid zai kore ki kuwa. Ai ku da gidan nan sai nan da wata tara. Hafsi ta sunkuyar da kai kasa cike da kunya. Haka suka zauna suna ta hira. Ko kadan basa barinta tayi kewar yan uwanta saboda yadda suke janta a jiki.

Tun daga bakin kofa yake jin kamshi mai dadi sai dai zuciyarshi wani irin kunci take masa. Yana shigowa falon yan uwansa suka fara tsokanarshi. Nafisa tace to ya isa haka ku tashi mu tafi. Duk suka yi mata sai da safe suka fita. Dama tun shigowarsa Hafsi bata yi masa magana ba saboda yadda su Hamida ke tsokanarta. jin bashi da niyyar kawar da shirun dake tsakaninsu tace masa ina yini. Lafiya ya amsa a takaice. Can ya sake cewa tashi mu shiga ciki muyi sallah ko. Dadi hakan yayi mata ta kara tabbatar da cewa Junaid ya fara maida hankali a lamuran addini. Fuskar nan tata a rufe ta bi bayansa. Suna shiga yaji hakurinsa ya soma karewa yace mata kiyi alwala ina zuwa nayi mantuwa a mota.

Cike da damuwa yake tuki ya rasa abinda ke masa dadi. Ace ya rasa abinda zaiyi ta tunani a yau sai Tilly, Why ??? Gidan ya nufa yayi saa suna zaune a falo. Mamaki karara a fuskar Tilly yace hado kayanki ki sameni a mota. Yana fita suka sa shewa da dariya. Tilly ta yi saurin dauko jaka ta watsa kaya kadan a jakar ko sallama babu ta fice. Rosie ta koma daki tana cin farar kasa wadda ta zame mata abinci yanzu. Mayen cikin yaki zubewa ita kuma tana tsoron wankin ciki.

Kusan awanni biyu kenan da fitarsa amma taji shiru. Tun tana sharewa har ta kasa hakuri. Lekowa tayi wajen gidan babu daya daga cikin motocin da yake shiga. Komawa tayi ta zauna tana ta sake sake. Gajiya tayi ta tashi tayi sallar isha da nafila ta zauna kan darduma tana karatu.

Hotel ya kama musu don yasan babu mai bashi mukullan gidan da Alhaji ya kama masa kafin ayi masa wani ginin inda zai iya hada matan biyu. Tilly ansha gyara ciki da waje. Ta nuna masa salo salo na kwarewarta a fanin shegantaka. Wayarsa ce tayi kara wurin shadayan dare. Har ya fara bacci Tilly ta dauka taga ansa H dear. Kashe wayar tayi gaba daya tayi  tsaki sannan da dariyar mugunta. Yarinya yau zaki bushe ta fada a fili..

Saroro ta tsaya kallon wayar. Yanzu ita Junaid ya kashewa waya? Ko tayi masa laifi ne? A falo ta kwana ranar tana kuka ita wannan wace irin rayuwa ce daga wannan sai wannan kullum. Ta yanke shawarar idan bai dawo ba da safe zata sanar da iyayensa.


Batul Mamman💖
Post a Comment (0)