TUN KAFIN AURE 37

TUN KAFIN AURE💐37




Hafsi da Ummati sun kusa rabin awa a waya suna ta shawarwari don yanzu kam Hafsi tasan bazata iya zama haka babu abokin shawara ba duk da cewa su Hamida suna iya kokarinsu. Yayarta Hadiza ma ta bugu sun dade suna magana. Tana wayar Nafisa ta shigo da wata karamar jaka a hannunta ta zauna kan kujera. Hafsi ta gama waya suka gaisa. Nafisa tace kanwata kinga yadda Allah Yake ta jarrabar mu da abubuwa kullum ko? Yauma hakuri dai zan kara baki. Da yar shawara kadan. Kinga wadanan kayan masu tsada ne amma fa idan kika sha baza ayi asarar kudin tara ba. Suna gyara mace sosai sannan ki rika shan fruits musamman kankana. Akwai kunun aya ma da ake hadawa da ita da cucumber, dabino, kaninfari, citta da kwakwa. Zan hada miki da kaina kafin anjima. Munyi magana da Mommy ke zaki fara tarewa sannan bayan sati daya talatu ta tare amma gidanta daban ne. Kiyi iya kokarinki ki zama tamkar karuwa kema a wurin mijinki kinga ya san wasu matan so raba shi da irinsu sai kin dage sosai. Kan Hafsi a kasa duk kunya ta kamata ta kasa magana. Nafisa ta nuna mata yadda zata yi amfani da kayan data kawo mata. Ke ni ki dena jin kunyata bazan taba bari matan banza su rabaki da mijinki ba. Tunda kika auri Junaid kin gama mana komai.

Talatu yar gidan Mal Jibo mai faskare amaryar Junaidu dan sanata. Kirari ne Rosie da ke zaune kan kujera take wa aminiyarta. Tilly tace yanzu fa dole inyi ta amsa sunan Talatu sunan dana manta dashi tun a kauye. Suka tafa sanan rosie ta miko mata kullin magani. Ga wanan kawata ki shafa  hannu ne ki taba shegen. Wallahi zaki sha mamaki don watarana ma sai ya gundireki idan ya fara like miki. Wata shewa suka yi tace Rosie ba kyau. Gara tun wuri na fara kiranki Samiranki kada ayi subutar baki a gaban surukai. Hakane, yanzu dai zan kira shi yazo a sunan kina zubar da jini sai ki fara gwada saarki. Bikin ma da akace muyi a garinmu zasu sha mamaki don sai munyi kara'i. Sake tafawa sukayi sannan Tilly wadanda sun koma dakin da Rosie ta kama musu ta dauki waya ta kira shi.

Tun safe ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda tsananin farinciki yau Hafsin sa zata tare. Ya fito daga wanka yaji karar waya a zatonsa ma Hafsi ce don tun dare take tsokanarshi da flashing. Tsaki yayi kamar tana gabansa daya  ga number din Tilly. Yana dauka Rosie ra kwarma ihu tace yazo Tilly tana ta zubar da jini. Wani tsakin yayi ya ajiye wayar ya cigaba da shiryawa. Sake buguwa suka yi har sau biyar sannan ya dauko a wulakance yace gani nan zuwa. Cikin gidansu ya shigo ya fadawa Mommy inda zashi. Ta tabe baki sai ka dawo. Kada dai ka dade yace to. Shi har a ce masa kada ya dade yadda yake zumudin nan.

Suna jin tsayuwar motarsa Tilly ta kwanta a kasa tana wai wai. Kudi ya jefa mata yana mata kallon banza gashi nan nasan abinda kike nema kenan. Ganin bashi da niyar taimaka mata ta tashi ta mike ta riko shi. Juni boy ka saki jikinka mana ai an riga an daura. Ina jiranka anjima kazo mu tafi namu gidan don a sannu zansa ka manta wannan kwailar. Hankadeta yayi har ta fadi kamar zaiyi magana ya fasa ya fice. Rosie dake kitchen ta fito da sauri tana mata sannu. Tilly tace aikin banza maganin naki baya komai ji yadda ya ture ni.



Batul Mamman💖
Post a Comment (0)