ISTIGHFARI YANA JANYO ALKHAIRI DA ALBARKA MAI YAWA SANNAN YANA TUNKUDE BALA'I

Manzon Allah ο·Ί baya sabon Allah saboda Allah ya bashi kariya da dukkan sabon Allah,sannan da zaiyi sabon Allah to Allah ya gafarta masa dukkan abinda zai aikata,amma duk da haka Manzon Allah ο·Ί yafi kowa yawaita Tuba da Istighafi da komawa zuwa ga Allah.
Manzon Allah ο·Ί yana cewa;-
*(Wallahi ina yin Istighfari ina tuba zuwa ga Allah ayini fiye da sau Saba'in....)*
A wata riwayr yana cewa:-
*(....Ina Tuba kuma ina neman gafarar Allah a yini sau dari...)*
Daya daga cikin Sahabban Manzon Allah ο·Ί yana cewa;-
*"Muna kirgawa Manzon Allah ο·Ί a wajan zama yana nemi gafara da istighfari zuwa ga Allah sau dari awajan zama guda daya".
Dan haka wajibine ga dukkan kowane bawa mai so da imani da koyi da Manzon Allah ya yawaita tuba da istighfari mai yawa.
Wani mutum ya shiga Wannan Babban Tabi'i wato Imam Hasan Albasary RHA,sai yace:
"Ya Imam Sama ta daina zubar da ruwanta,sai Imam yace;-
*"Kuje ku yawaita yin Istighfari"*.
Sannan wani mutum ya shiga wajansa yace:Ya Imam Matata bata haihuwa,sai Imam yace masa;-
*"Kuje ku yawaita Istighfari mai yawa"*.
Sannan sai wani mutum na ukku yace ;Ya Imam ina fama da Talauci mai yawa,sai Imam Yace;-
*"Ka yawaita yin Istighfari:*sai daya daga cikin Dalibansa yace da shi,Abin mamaki a gareka ya Imam,mutane guda ukku sun shigo suna tambayarka akan abubuwa daban daban amma duka kana basu amsa da su yawaita Istighfari??
Sai Imam Hasanul Basary yace da shi;-
*"Shin baka karanta fadin Allah Ta'ala ba
﴿ΩَΩُΩْΨͺُ Ψ§Ψ³ْΨͺَΨΊْΩِΨ±ُΩΨ§ Ψ±َΨ¨َّΩُΩ ْ Ψ₯ِΩَّΩُ ΩَΨ§Ωَ ΨΊَΩَّΨ§Ψ±Ψ§ً * ΩُΨ±ْΨ³ِΩِ Ψ§ΩΨ³َّΩ َΨ§Ψ‘َ ΨΉَΩَΩْΩُΩ ْ Ω ِΨ―ْΨ±َΨ§Ψ±Ψ§ً *ΩَΩُΩ ْΨ―ِΨ―ْΩُΩ ْ Ψ¨ِΨ£َΩ ْΩَΨ§Ωٍ ΩَΨ¨َΩِΩΩَ ΩَΩَΨ¬ْΨΉَΩْ ΩَΩُΩ ْ Ψ¬َΩَّΨ§Ψͺٍ ΩَΩَΨ¬ْΨΉَΩْ ΩَΩُΩ ْ Ψ£َΩْΩَΨ§Ψ±l)*
Fassara;-
*{"Shi na ce,'Ku nαΊ½mi gΓ£fara daga Ubangijinku,lalle ne shi Ya kasance Mai gΓ£fara ne."Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ΙuΙΙuga.""Kuma ya yalwata muku game da dΕ©kiya da Ιiya, Ya sanya muku (albarka) ga gΓ΅naki,kuma Ya sanya muku koguna}*
Allah yana cewa:-
﴿ΩَΩَΨ§ ΩَΩْΩ ِ Ψ§Ψ³ْΨͺَΨΊْΩِΨ±ُΩΨ§ Ψ±َΨ¨َّΩُΩ ْ Ψ«ُΩ َّ ΨͺُΩΨ¨ُΩΨ§ Ψ₯ِΩَΩْΩِ ΩُΨ±ْΨ³ِΩِ Ψ§ΩΨ³َّΩ َΨ§Ψ‘َ ΨΉَΩَΩْΩُΩ ْ Ω ِΨ―ْΨ±َΨ§Ψ±ًΨ§ ΩَΩَΨ²ِΨ―ْΩُΩ ْ ΩُΩَّΨ©ً Ψ₯ِΩَΩ ΩُΩَّΨͺِΩُΩ ْ ΩَΩَΨ§ ΨͺَΨͺَΩَΩَّΩْΨ§ Ω ُΨ¬ْΨ±ِΩ ِΩΩَ ﴾
Fassara;-
*("Kuma,ya mutΓ£nena! Ku nαΊ½mi Ubangijinku gΓ£fara,sa'an nan kuma ku tΕ©ba zuwa gare Shi,zai saki ruwa sama a kanku, tanΓ£ mai yawan zubar da ruwa,kuma Ya ΖΓ£ra muku wani Ζarfi ga Ζarfinku. Kuma kada ku jΕ©ya kunΓ£ mΓ£su laifi)*.
@ΩΩΨ―: 52.
Ψ§ΩΨ₯Ω Ψ§Ω Ψ§ΩΩΨ±Ψ·Ψ¨Ω Ψ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΩΩ -:
Yana cewa:-
*"Yana daga cikin falalar istighfari da Tuba,Allah baku abinda da ya hanaku na ni'imarsa tare da yalwata maku arziqi mai yawa da albarka mai yawa"*.
@Ψ§ΩΨ¬Ψ§Ω ΨΉ ΩΨ£Ψ£ΨΩΨ§Ω Ψ§ΩΩΨ±Ψ’Ω( 9-2 ).
Allah ne mafi sani.
*Allah muna rokonka da sunayenka mafiya kyawu da siffofinka mafiya kamala da daukaka,Ya Rabbi Ya Rabbi ya Allah kayi rahama da gafara da afuwa ga dukkan musulmin duniya baki daya masu rai da wadanda suka rigamu gidan gaskiya tun daga Annabi Adam har zuwa yanzu,Amin Amin Amin ya Allah*.
Manzon Allah ο·Ί baya sabon Allah saboda Allah ya bashi kariya da dukkan sabon Allah,sannan da zaiyi sabon Allah to Allah ya gafarta masa dukkan abinda zai aikata,amma duk da haka Manzon Allah ο·Ί yafi kowa yawaita Tuba da Istighafi da komawa zuwa ga Allah.
Manzon Allah ο·Ί yana cewa;-
*(Wallahi ina yin Istighfari ina tuba zuwa ga Allah ayini fiye da sau Saba'in....)*
A wata riwayr yana cewa:-
*(....Ina Tuba kuma ina neman gafarar Allah a yini sau dari...)*
Daya daga cikin Sahabban Manzon Allah ο·Ί yana cewa;-
*"Muna kirgawa Manzon Allah ο·Ί a wajan zama yana nemi gafara da istighfari zuwa ga Allah sau dari awajan zama guda daya".
Dan haka wajibine ga dukkan kowane bawa mai so da imani da koyi da Manzon Allah ya yawaita tuba da istighfari mai yawa.
Wani mutum ya shiga Wannan Babban Tabi'i wato Imam Hasan Albasary RHA,sai yace:
"Ya Imam Sama ta daina zubar da ruwanta,sai Imam yace;-
*"Kuje ku yawaita yin Istighfari"*.
Sannan wani mutum ya shiga wajansa yace:Ya Imam Matata bata haihuwa,sai Imam yace masa;-
*"Kuje ku yawaita Istighfari mai yawa"*.
Sannan sai wani mutum na ukku yace ;Ya Imam ina fama da Talauci mai yawa,sai Imam Yace;-
*"Ka yawaita yin Istighfari:*sai daya daga cikin Dalibansa yace da shi,Abin mamaki a gareka ya Imam,mutane guda ukku sun shigo suna tambayarka akan abubuwa daban daban amma duka kana basu amsa da su yawaita Istighfari??
Sai Imam Hasanul Basary yace da shi;-
*"Shin baka karanta fadin Allah Ta'ala ba
﴿ΩَΩُΩْΨͺُ Ψ§Ψ³ْΨͺَΨΊْΩِΨ±ُΩΨ§ Ψ±َΨ¨َّΩُΩ ْ Ψ₯ِΩَّΩُ ΩَΨ§Ωَ ΨΊَΩَّΨ§Ψ±Ψ§ً * ΩُΨ±ْΨ³ِΩِ Ψ§ΩΨ³َّΩ َΨ§Ψ‘َ ΨΉَΩَΩْΩُΩ ْ Ω ِΨ―ْΨ±َΨ§Ψ±Ψ§ً *ΩَΩُΩ ْΨ―ِΨ―ْΩُΩ ْ Ψ¨ِΨ£َΩ ْΩَΨ§Ωٍ ΩَΨ¨َΩِΩΩَ ΩَΩَΨ¬ْΨΉَΩْ ΩَΩُΩ ْ Ψ¬َΩَّΨ§Ψͺٍ ΩَΩَΨ¬ْΨΉَΩْ ΩَΩُΩ ْ Ψ£َΩْΩَΨ§Ψ±l)*
Fassara;-
*{"Shi na ce,'Ku nαΊ½mi gΓ£fara daga Ubangijinku,lalle ne shi Ya kasance Mai gΓ£fara ne."Ya sako (girgijen) sama a kanku da ruwa mai ΙuΙΙuga.""Kuma ya yalwata muku game da dΕ©kiya da Ιiya, Ya sanya muku (albarka) ga gΓ΅naki,kuma Ya sanya muku koguna}*
Allah yana cewa:-
﴿ΩَΩَΨ§ ΩَΩْΩ ِ Ψ§Ψ³ْΨͺَΨΊْΩِΨ±ُΩΨ§ Ψ±َΨ¨َّΩُΩ ْ Ψ«ُΩ َّ ΨͺُΩΨ¨ُΩΨ§ Ψ₯ِΩَΩْΩِ ΩُΨ±ْΨ³ِΩِ Ψ§ΩΨ³َّΩ َΨ§Ψ‘َ ΨΉَΩَΩْΩُΩ ْ Ω ِΨ―ْΨ±َΨ§Ψ±ًΨ§ ΩَΩَΨ²ِΨ―ْΩُΩ ْ ΩُΩَّΨ©ً Ψ₯ِΩَΩ ΩُΩَّΨͺِΩُΩ ْ ΩَΩَΨ§ ΨͺَΨͺَΩَΩَّΩْΨ§ Ω ُΨ¬ْΨ±ِΩ ِΩΩَ ﴾
Fassara;-
*("Kuma,ya mutΓ£nena! Ku nαΊ½mi Ubangijinku gΓ£fara,sa'an nan kuma ku tΕ©ba zuwa gare Shi,zai saki ruwa sama a kanku, tanΓ£ mai yawan zubar da ruwa,kuma Ya ΖΓ£ra muku wani Ζarfi ga Ζarfinku. Kuma kada ku jΕ©ya kunΓ£ mΓ£su laifi)*.
@ΩΩΨ―: 52.
Ψ§ΩΨ₯Ω Ψ§Ω Ψ§ΩΩΨ±Ψ·Ψ¨Ω Ψ±ΨΩ Ω Ψ§ΩΩΩ -:
Yana cewa:-
*"Yana daga cikin falalar istighfari da Tuba,Allah baku abinda da ya hanaku na ni'imarsa tare da yalwata maku arziqi mai yawa da albarka mai yawa"*.
@Ψ§ΩΨ¬Ψ§Ω ΨΉ ΩΨ£Ψ£ΨΩΨ§Ω Ψ§ΩΩΨ±Ψ’Ω( 9-2 ).
Allah ne mafi sani.
*Allah muna rokonka da sunayenka mafiya kyawu da siffofinka mafiya kamala da daukaka,Ya Rabbi Ya Rabbi ya Allah kayi rahama da gafara da afuwa ga dukkan musulmin duniya baki daya masu rai da wadanda suka rigamu gidan gaskiya tun daga Annabi Adam har zuwa yanzu,Amin Amin Amin ya Allah*.