RUBUTACCIYAR WAƘAR UBAN GIDA NA


UBAN GIDA NA

Aminu Ladan Abubakar Alan WaΖ™a 
Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena x2

In banda bautar zuciya da bata tserarwa,
Ya za na tara abincin da bani cinyewa?
Ya za na gina gida wanda ba shi Ι—orewa?
Ya za na tara Tufafin da bani sanyawa?
Ya za na dasa hasashen da ba shi Ι—orewa?
Ya za na shimfiΙ—a daula da bata Ι—orewa?
Ya za na Ι—aura majanyin da za ya suncewa?
Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, da kayi gyara kafin a gincire kwana...

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

 Iyye... In banda bautar zuciya da ke halakarwa,
Abin hawa na ya zarce na hawan kowa
Rigar sakawa ta zarce ta jikin kowa
Gami da takalma sun fi na Ζ™afar kowa
Dangi agogona ya fuce na gun kowa
Daidai da zobena yafi hasashen kowa 
Hatta da birona alΖ™alam na zanawa 
Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, wallahi da an gyara da tsakiyar rana... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Hmm... Gida dubu na gina tanadin wajen kwana 
Ciki da falo dubbai daban-daban Ι—ana 
Don tanadi na talauci da ke tsumin rana
Sannan in kaucewa idanduna da ke bina 
In Ι“adda sawayena ga masu biko na 
An Ι—auki duniya mai tabbata gidan kwana 
Gida ga mai burin rayuwa gidan Ζ™una 
Ya mai gida na da zaka duba zance na, wallahi Allaah da ka cikan Muradina.. 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Iyye... Mun zama bayi na ciki da ba shi turewa 
Muna haΖ™a ya na mai rijiya da babu ruwa 
Muna nutsewa Ζ™asa zuciya tana Ζ™wawa 
Muna ta bautar gangar jikinmu ba Ζ™iwa 
Muna biye al'aura muna Tsiyacewa 
Giya ta rai ta sanya mu Ζ™ara ruΙ—ewa 
Ina tunani da sani da ke a Ζ™waΖ™walwa? 
Uwargidana da kin fahimci zance na, wallahi Allaah da an rufe tunanina... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Ni zuciyata kuma ta hanani yin barci 
Dare da rana kuma ba ragi na sassauci 
Tana ta kakabi ko abinci bata ci 
Cikinta mamaki ya game ta ga Ζ™unci 
Sannan tunani yayi tarnaΖ™i gadon barci 
Ina ta mamaki kan hali na zalunci 
BaΖ™in maciji da ake kira da Kumurci 
Uban gida na bisa Ζ™arΖ™ashin tunanina, ya fi mu jin gantsar nasa a tunanina... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Duk inda ka ga Ζ™asa country a Ilimina 
To arzikin da buwayi ya basu dangina 
Ya zarce dukka buΖ™atu nasu da an tona 
Sai dai idan jagoransu ya zamo Ι“auna 
Sai babu adalci gunsu shugabannina 
Idan da adalci babu mai shiga rana 
Kowansu ya zarce wajibinsa dangina 
Ya shugabana in an nazar a zance na, wallahi Allaah Ya tseratar da mu Ζ™una... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Hannunka mai sanda yau nake iyayena 
Nuni da NishaΙ—i ne nake wa babana 
Yau gyara kayanka ba shi maida mu rana 
Ya shugabana in har ka Ι—auki zance na 
Abinda ka tara ka aje gidan kwana 
Da wanda ka yi bushasha kake tsumin Ζ™auna 
To wanda ka bayar za shi yayi ma rana 
Uban gida na in yanzu kaga laifi na, ai zaka gane ran tsai da mu cikin rana... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena 

Ku taimaka mini gun dakatar da kuka na
Don kar na Ζ™arar da ruwan cikin idanuna 
Suna da rana a gaba zubar hawaye na 
Wai shin ko ruhi da jiki da hankali Ι—ana 
Sun yarda ranar tsayuwa tana tsumin kwana? 
Wai shin ko labari na wuta da Aljannah
Anya bani adama ya aminta ko Ι—ana? 
Ya shugabana da ka amince zance na, me za ya ruΙ—e ka da handama tsakar rana... 

Ubangijina Afuwar Ka ni nake nema.... 
Ubangijina gafarar Ka ni nake nema 
Ubangijina Afuwar Ka mu muke nema 
Ubangijina sauΖ™in Ka ne abin nema 
Ubangijina Rahamar Ka mu muke nema
Ubangijina gafarar Ka mu muke nema 
Ubangijina Ceton Ka mu muke nema... 

Uban gida na da zaka Ι—auki zance na, Aradu Allaah da ka haye hasashena X2
Post a Comment (0)