SHIN ZAN IYA SALLAR IDI A GIDA?


SHIN ZAN IYA SALLAR IDI A GIDA!!!
Haƙiƙa malamai sunyi sabani akan wannan mas'alar zuwa gida biyu:
Na farko: Wanda suke ganin halascin yin hakan wanda sune mafi yawan malamai (Jumhuur) Kamar Imani Malik, Shafi'i da Ahmad Bin Hanbal Allah ya jiƙansu.
Na biyu: masu ganin bai halasta ba kamar Imamu Abu Hanifah.
Ga kaɗan daga maganganun Malamai akan Mas'alar:
Al'Imamul Kharshi (Malikiyyah) yana cewa:
وقال الخرشي (مالكي) : "يستحب لمن فاتته صلاة العيد مع الإمام أن يصليها ، وهل في جماعة , أو أفذاذا ؟ قولان" انتهى باختصار من "شرح الخرشي" (2/104).
Anso ga wanda sallar Idi ta kubuce masa tare da liman da ya sallaceta, amma shin zasu yi jam'i ne ko kuma kowa zai yi nashi ne? Akwai maganganu biyu.
Haka Al'imamul Muzani(Shafi'iyyah) ya naqalto daga Al'imamus Shafi'i cewa:
نقل المزني عن الشافعي رحمه الله في "مختصر الأم" (8/125) : " ويصلي العيدين المنفرد في بيته والمسافر والعبد والمرأة " انتهى .
Mutum zai iya sallatar Idi guda biyu shi kaɗai a gidansa haka ma matafiyi ko bawa ko mace.
Ibnu Qudama (Hanabila) ya fada a cikin littafinsa Almugni:
"وهو مخير ، إن شاء صلاها وحده ، وإن شاء صلاها جماعة" انتهى
An baiwa mutum zaɓi game da sallar idi, in yaso ya sallaceta shi kaɗai ko yayi ta a jam'i. Ma'ana ga wanda ta kuɓuce masa tare da liman.
Haka ma Almardawi (Hanabila) yana cewa a cikin littafinsa Al'insaf:
"وإن فاتته الصلاة (يعني : صلاة العيد) استحب له أن يقضيها على صفتها (أي كما يصليها الإمام)" انتهى
Idan sallah ta kubuce masa, yana nufin sallar idi, anso ya rama ta irin yadda ake yinta tare da liman.
Amma kamar yadda na ambata a farko cewa akwai masu ganin rashin halascin hakan, zan yi ishara zuwa ɗaya daga cikin maganganun su.
Yazo a cikin littafin Addurarul Mukhtar a Hashiyar ibnu Abideen (Hanafi):
وفي الدر المختار مع حاشية ابن عابدين (2/175) (حنفي) : " ولا يصليها وحده إن فاتت مع الإمام "
Ba zai sallaceta (idi) shi kaɗaita ba idan ta kubuce masa tare da liman.
Babban Kwamitin fatawa na ƙasar Saudiyya (اللجنة الدائمة) sun baya fatawar halascin hakan
وجاء في فتاوى اللجنة الدائمة للإفتاء (8/306) : "صلاة العيدين فرض كفاية؛ إذا قام بها من يكفي سقط الإثم عن الباقين .
ومن فاتته وأحب قضاءها استحب له ذلك، فيصليها على صفتها من دون خطبة بعدها، وبهذا قال الإمام مالك والشافعي وأحمد والنخعي وغيرهم من أهل العلم. والأصل في ذلك قوله صلى الله عليه وسلم : (إذا أتيتم الصلاة فامشوا وعليكم السكينة والوقار فما أدركتم فصلوا وما فاتكم فاقضوا) ، وما روي عن أنس رضي الله عنه أنه كان إذا فاتته صلاة العيد مع الإمام جمع أهله ومواليه، ثم قام عبد الله بن أبي عتبة مولاه فيصلي بهم ركعتين، يكبر فيهما. ولمن حضر يوم العيد والإمام يخطب أن يستمع الخطبة ثم يقضي الصلاة بعد ذلك حتى يجمع بين المصلحتين . وبالله التوفيق وصلى الله على نبينا محمد وآله وصحبه وسلم " انتهى .
اللجنة الدائمة للبحوث العلمية والإفتاء
الشيخ عبد العزيز بن عبد الله بن باز ، الشيخ عبد الرزاق عفيفي ، الشيخ عبد الله بن غديان.
والله أعلم .
Ma'ana duk wanda idi ya kubuce masa kuma yana so so ya rama to mustahabbi hakan, wannan shine maganar Imamu Malik, Shafi'i, Ahmad, Nakha'i da wasunsu. Dalili akan hakan shine hadisin idan zaku jewa sallah to kuje a natse, abinda kuka riska ku sallaceshi wanda kuma ya kuɓuce muku ku rama, da kuma abinda aka ruwaito daga Anas ɗan Malik R.A cewa idan Idi ya kuɓuce masa yana tara iyalansa da bayinsa suyi raka'a biyu.
Har ila yau babban Majalisar Malamai na ƙasar Misra dake Azhar sun yi fatawar halascin yin sallar idi a gida musamman a wannan lokaci da muke na bazuwar annobar corona virus. Ga abinda fatawar ke cewa:
"كبار العلماء": يجوز أداء صلاة العيد في البيت.. والخطبة ليست شرطاً
أصدرت هيئة كبار العلماء بالأزهر برئاسة فضيلة الإمام الأكبر أ.د/ أحمد الطيب، شيخ الأزهر الشريف، اليوم الأحد، بيانًا للمسلمين حول العالم بشأن الأحكام المتعلقة بصلاة العيد في ظل استمرار تفشي فيروس "كورونا المستجد"، انطلاقًا من مسئوليتها الشرعية وواجبها الديني.

وقالت الهيئة في بيانها، إنه يجوز أداء صلاة عيد الفطر المبارك في البيوت، بالكيفية التي تُصلى بها صلاة العيد، وذلك لقيام العذر المانع من إقامتها في المسجد أو الخلاء، ويجوز أيضا أن يُصليها الرجل جماعة بأهل بيته، كما يجوز أن يُؤدِّيها المسلم منفردًا، وذلك انطلاقا من أن أعظم مقاصد شريعة الاسلام حفظ النفوس وحمايتها ووقايتها من كل الأخطار والأضرار.
أوضحت الهيئة أنه لا تشترط الخطبة لصلاة العيد، فإن صلى الرجل بأهل بيته فيقتصر على الصلاة دون الخطبة، مؤكدة أنه إذا صلى المسلم صلاة العيد منفردًا أو جماعة بأهله في بيته، فإنه يصليها ركعتين وبالتكبيرات الزوائد، وعدد التكبيرات الزوائد سبع في الركعة الأولى بعد تكبيرة الإحرام، وخمس في الركعة الثانية بعد تكبيرة القيام إلى الركعة الثانية، مضيفة أن وقت صلاة العيد هو وقت صلاة الضحى، يبدأ من بعد شروق الشمس بثلث ساعة ويمتد إلى قبيل أذان الظهر بثلث ساعة، فإن دخل وقت الظهر فلا تصلى؛ لأن وقتها قد فات.

ودعت هيئة كبار العلماء بالأزهر، المسلمين في مشارق الأرض ومغاربها، إلى التضرع إلى الله في هذه الأيام المباركة بالدعاء لرفع ما حل بالإنسانية من البلاء، وأن يُسارعوا لفعل الخيرات والإكثار من الصدقات ومساندة المرضى والمعوزين، تخفيفًا لما حل بهم من آثار هذا الوباء، داعين الله أن يرفع البلاء عن الإنسانية كلها، وأن يحفظ بلادنا والناس جميعًا من هذا الوباء، ومن جميع الأمراض والأسقام.
A takaice sunce ya halasta yin sallar idi a gida irin yadda ake yinta tare da liman, kuma mutum zai iya yi shi kaɗai ko tare da iyalansa, zai yi raka'a biyu tare da ƙarin kabarbari da ake yi. Kabarbari bakwai a raka'ar farko bayan kabbarar harama, da kabarbari biyar a raka'a ta biyu bayan kabbarar miƙewa daga sunada. Kuma ba sharaɗi bane sai anyi khiɗuba, sannan zai yi ta lokacinta wato daga hantsi har zuwa lokacin zawali.
Daga ƙarshe Majalisar tayi kira ga Musulmai a ko ina a duniya da su yawaita addu'oi tare da ƙanƙantar da kansu zuwa ga Allah da neman ya yaye mana wannan hali da muke ciki.

A bisa wannan bayanai nake kira ga yan'uwa musulmi musamman waɗanda suke a jihohi da aka hana tarurruka da ayi a gabatar da wannan ibadar a gidajenmu tunda hakan ya halasta mu roƙi Allah ya yaye mana damuwarmu.
Allah ya taimake mu
Post a Comment (0)