YADDA ƊAKIN MA'AURATA YA KAMATA YA KASANCE A LOKACIN SADUWA

*SIRRIN MALLAKAN MIJINKI*

*_Yadda Ya Kamata Dakin Ma'aurta Ya Kasance A Lokacin Saduwa_*

Ya kamata dakin ma'aurata ya kasance kamar haka; A duk yayin da suka nufi saduwa da junansu a cikin dare ne ko rana. Kamar yadda sunnar Manzon Allah ta tsara kamar haka;

1. Dakin ya kasance babu wani mutum a cikin ko da yaro ne.

2. Daki ya kasance a lokacin mai nutsuwa.

3. A samu karancin mutane a kusa da wajen.

4. Dakin ya kasance a kulle yake.

5. Sannan a kashe fitilar cikin dakin.

6. Abin kwanciyar ya kasance ba mai motsi ba.

7. Dakin da abin kwanciyar su kasance mafi dadin kamshi.

8. Ma'aurata su kwanta a tube ba tare da tufafi ba, amma ba laifi ba ne in sun kwanta da kaya a jikinsu.

9. Su kwanta a cikin mayafi guda daya, amma ba laifi ba ne in sun kwanta a mayafi daban-daban.

10. Su ambaci sunan Allah kafin su fara saduwa.

11. Daki ya kasance ba hayaniya.

Wabillahi Taufiq.
Rubutawa: *Abu Imam (Auwal Abdullahi)*

Gabatarwa: *Abu Imam (Auwal Abdullahi)*


*- Zauren Macen Kwarai-*

*. Ga masu buqatar shiga Zauren Macen Kwarai sai a turo da cikakkiyar sallam tare da cikakken suna da Address ta wannan Number +2348036692586,08062828025 a WhatsApp.*

Post a Comment (0)