SALAFUS SALEH 01

SALAFUS SALEH 
 
📌 (001) 
 
Abdullahi Ibn Mas'ud (Allah Ya kara Masa yarda) yace: 
 
"Dukkan wanda ya gyara tare da kyautata É“oyen sa, to Allah zai kyautata tare da gyara masa bayyanan sa, duk wanda ya gyara alaÆ™ar sa tsakanin sa da Allah, to Allah zai gyara masa alaÆ™ar dake tsakanin sa da Mutane". 
 
Wannan fa'ida an ruwaito ta daga Magabata manya guda biyu, an ruwaito ta daga Ibn Mas'ud R.A da kuma Sufyanu Bn Uyaina Allah yayi musu rahama, kamar yadda yazo cikin waÉ—an nan littafai: 
Ibnu Abid-dunya a cikin Littafin Al-Ikhlas, da 
Al-Iman na Ibnu Taimiyah 
 
A taÆ™aice wannan Fa'ida tana koyar da mu abubuwa guda biyar: 
 
1- Aiyukan Bawa na É“oye sun fi matsayi da daraja fiye da aiyukan sa na bayyane a wajan Allah.  
 
2- Allah yana yiwa Bawa sakamako gwargwadon yadda yayi aiki da kuma irin aikin sa.  
 
3- Mu kiyaye dokokin Allah a fili da É“oye, wannan itace hanyar samun Aljanna mafi girma.  
 
4- Babbar alamar jin tsoron Allah itace: Mutum yafi kyautata aiyukan sa na É“oye fiye da yadda zai yi su a fili a gaban jama'a. 
 
5- Ana samun matsayi da yardar Mutane ne ta hanyar kyautata alaÆ™a tsakanin ka da Allah. 

✍ ANNASIHA TV
(https://t.me/annasihatvchannel)

Post a Comment (0)