YAREN SOYAYYA 1


*💝🌹YAREN SOYAYYAH🌹💝 // 01*
 .
Rubutawa: Dr. Abdulkadir Ismail

          *_SHIMFIDA_*
Godiya gaba dayanta Allah ne ya cancance ta, muna gode masa muna neman gafararsa, kuma muna neman taimakonsa. Dacensa da shariyarsa da yardan sa su ne babban rabo, tabar barewar'sa da rashin taimako daga gare shi ita ce babbar hasara. Salati da sallama ga masoyinsa, abin Qaunar mu annabi Muhammad, ya shiryar damu zuwa ga han-yar tsira, ya isar da sako kamar yadda Allah ya umarce shi, ya koma ga Ubangijinsa bayan ya isar da amanar da aka daura masa, Allah yayi dadin tsira da aminci da sallama gare shi da iyalansa da sahabbansa da duk wanda sukabi tafarkinsa har izuwa ranar Qar'she.
.
Aure shi ne ginshikin Samar da zuri'a tagari a addinin musulunci, kuma wan-zuwarsa al'amari ne da wannan addinin, ta hanyoyi daban-daban ya lazimta a kula da shi, lalacewarsa abin ki ne kyama matukar ba lalura bace Mai kar'fin gaske ta wajabta hakan ba. Manzon Allah ya yi umar'ni da a auri mace wadda ake qauna, kuma take tarairayar mutum da kauna. Anas dan Malik yace:
يٱمرنا بالباءة، وينهانا عن التبتل نهيًا شديدًا ويقول: تزوجوا الودود الولود". 
Manzon Allah ﷺ ya kasnce yana umartar'mu da yin aure, kuma yana hana mu hani mai tsanani ga kin yin aure, kuma yana cewa: "Ku auri ( Mata ) masu son ku kuma masu haihuwa". Ma'anar "Wadud" ita ce wanda take son mutum kuma take yin abin da zata janyo hankalinsa ya so ta.
.
Mafi yawancin lokuta aure yana kasancewa ne a bisa soyayyah, wani lokacin ma'aurata sukan iya baje turjiyar da a kan samu daga wajen magabatansu wadanda ba lallai su kasance cikin farin ciki da haduwar ba, wani lokacin turjiyar masoyan kan sanya a yi baran-baran tsakanin iyaye da `ya`ya. Amma kwatsam! Ba tare da an dauki shekaru ba, sai a ga auren yana reto, ko ya sane, ko yana neman tabar-barewa ma baki daya, ko ma an rabu ta hanyar saki, kuma ba tare da wannan soyayyar da aka yi a farko ta iya tabuka wani gudunmawa wajen ceto auren ba .
.
Wannan yakan sa mutane da yawa su yawaita tambayar cewa: me ke faruwa ga soyayya ne bayan an yi aure? Ko dama soyayyar ba ta Allah da Annabi ba ce?
  Ko kuwa ma asalin soyayya da ake fada duk zancen kawai ne ba shi da wani tushe ballantana makama?
  Idan kuwa haka ne, to meyasa Manzon Allah ﷺ Zai yi umarni da a yi aure da soyayyah?
Kuma me yasa har ya raba auren wata da ta nuna cewa tilas aka yi mata da wanda ba ta so?
.
Ko kuwa asiri ake yi dan samar da soyayyah, kuma yake karyewa bayan an yi aure?
  Ko kuwa akwai dai wani abu da ya boyu ga masoyan wanda idonsu yake rufewa a kansa lokacin neman aure, amma sai su ga ya canja bayan yin auren?
  Ko kuwa rashin dawwamar soyayya abu ne da yake cikin jinin hausawa da wadan da suke kewaye da su, ba haka abun yake ba a sauran kabilu na duniya?
.
Wannan dan littafi zai yi kokari ne ya bayyana abin da yake faruwa na rashin gane al'amura yadda ya kamata, tsakanin masoya bayan sun yi aure, zai tattauna wannan al-amari ne ta mahangar shari'ah tare da yin la`akari da masana ilimin halayyar dan Adam suka bayyana game da dabi'ar mutum.   
  Sannan kuma ya yi bayanin wasu matakai da suke dawwamar da soyayyah bayan aure, su kawo fahimtar juna, da janyo hankalin juna don sanya marari ga juna. 
.
  Shi wannan littafi ba wani sabon abu zai kawo ba wanda Malamai da masana ba su yi magana a kansa ba, amma dai zai rattabo shi ne ta wani tsari da watakila mai karatu bai san haka suke kasancewa ba, wani lokacin masana halayyar dan Adam da za a dauko daga cikin abubuwan da Allah ya sanar da su ba lallai su zama Musulmi ba, amma dai Allah cikin baiwarsa yana sanar da wanda ya so abin da ya so, aikin mumini a nan shi ne ya yi amfani da hikima duk inda ya same ta kamar yadda aka ce: 

"الحكمة صالة المؤمن يٱخذها إذا وحدها"

"Hikima abu ne na mumini da ya bata, duk inda yaga abin sa sai ya dauka". 
.
  Muna rokon Allah cikin ludufinsa ya sanya dace a cikin wannan rubutu, kuma ya mikar da karkata a duk inda za ta zo, ya kuma yi budi da fatahi a cikin abin da za a rubuta, domin idan bai ba da dama ba, babu wani abu da zai wakana.
Post a Comment (0)