WAƘAR ZAIDU IBRAHIM BARMO

ZAIDU IBRAHIM BARMO

Da sunan Rabbana zan fara waƙar Zaidu
Kogin maliya babu mai ganin ƙarshenka. 

Ɗa wurin Ibrahima na layin su Sa'idu
Gwarzonmu a yau muna maka sam-barka. 

Tsira gurin manzonmu wanda ya hana daudu
Kuma shi yazo da sallah yace kar mu yi shirka. 

Kun san mata su ke amfani da tandu
Shi ɗan jibiyawa ko sai dai waraƙa 

In ko rubutu kake so ka je gun Zaidu
Ko ma ba ka iya ba to za ya koya maka. 

Ƙimarsa ta zarce arewa har ta je ga kudu
Watarana duniya ƙwarai za ta yabe ka. 

Maƙiyanka da sun gane ka sai dai su gudu
Murhu da garwashi to wai wa zai taka? 

Masu yi maka hassada suna ruwa kai ko a tudu
Ka yi musu nisa babu mai iya kamo ka. 

Allah kare ka alfarmar Mahamudu 
Ya sa ka zamo a saman maƙiyanka. 

Ana maganar buhu wa ke zancen mudu? 
Kai me gayyar tsiya tafi abinka. 

Ka taka ka rausaya malam Zaidu
A MZM mun sani fa sam ba tamkarka

Allahu ya kiyasheka kamun gafiyar ɓaidu
Ya sa ka zamo cikin ni'ima a kabarinka.

Amin.

©️✍🏻
 Jamilu Abdulrahaman
   (Mr. Writer) 
  08185819176 
Haimanraees@gmail.com

Post a Comment (0)