*TASKAR TARIHI [24]*
```πΖangaren maganar Annabi gameda Yarjejeniyar Komai da ruwanka inda yace: ❝wannan Yarjejeniyar tafi mun daΙi da soyuwa a Zuciya ta fiye da in samu Jajayen RaΖuma, da za’a kiraye ne zuwa ga irin wannan aiki na alheri a Musulunci dana amsa``` ❞.
1⃣ Lallai Musulmi Adili ne mai tsaida Gaskiya ne koda tareda abokin husumar shi ne mas'ala ta kama, ka dubi Annabi Muhammad SAW yazo ne don ya tunkari wannan Jahiliyyah da tayi katutu a Ζasar Larabawa, amma bai mata Adawa da Ζiyayya a dunΖule da kuma a ΙeΙewarta ba (ba komai ne nasu ya yaΖa ba), har hakan yasa yazo yana musun abubuwan Alheri dake cikinta ba, a'a sai dai ma duk wani aikin alheri dake ga ita ya yabe shi ne, kuma Annabi yayi furuci da Daraja ga masu ita, koda kuwa sun kasance abokan husumar shi ne, kai koda ma sun kasance suna bayyana Ζiyayya da yaΖar shi Ζarara, kaji dai Annabi SAW yana yabon irin wannan Yarjejeniya.
Annabi yayi mana haka ne don ya nuna mana mu kasance masu adalci tareda abokan husumar mu, sannan kuma gaskiyar dake tare da waΙansun mu mu karΙe ta, kada Adawa ta tunkuΙa mu muΖi fahimtar alherin dake tattare da abokan husumar mu❗️.
Shi Manzon Allah SAW cewa ma yake yi: ❝Ni an aiko ni ne don in cika Kyawawan Ζabi'u❞, anan Annabi yana ce mana: a Jahiliyya akwai kyawawan Ιabi’u, Shi yazo ne don ya cika su, kuma don ya Ζarasa su, Manzon Allah bai yi inkarin Ιabi'u kyawawa waΙanda suke dasu ba, saboda kaΙai sun nuna mishi Ζiyayya kuma sun yaΖe shi; don haka ake Nasiha ga Musulmi ya zama Adili, mutumin kirki, mai faΙin gaskiya tare da wanda yake husuma dashi.
Shi dai Adalci da tsayawa gaskiya, abun nema ne wanda wasu daga cikin Mutane sun gafala a wajen mu'amalar su tare da waΙanda suka saΙa musu, abunda yakai suke gafala suyi Ζememe basa iya faΙan wani alheri dake tattare da abokin adawar su, ko kuma duk wani saΙani dake tsakanin su.
Wannan kuma baya nufin baza'a ambaci kuskuren Mutum ba don tsoratarwa, ba haka ake nufi ba, babu makawa dole a bayyana kuskuren mutum, saboda tsoratarwa daga wannan kuskure, don kada wanin shi ya afka cikin wannan kuskure, sai dai ma wannan na daga cikin Babin umarnin da kyakkyawa da hani daga mugun abu da yake faruwa.
2⃣ Al'amarin da zamu sake fahimta anan, shi dai Musulmi mai kira ne zuwa ga alheri, don haka yana taimakawa duk wani wanda yake kira zuwa ga alheri, domin asalin shi Musulmi shi yafi dacewa da alheri, duk wanda yayi kira zuwa ga wani alheri ga zamantakewar Al'ummah; to Musulmi ya kamata ya zama mai taimako gareshi.
Ya kai Musulmi! Idan kaga wani yana kira zuwa ga wani alheri da za'a kawowa zamantakewa ko Gari na Musulmi, ko kuma wannan abun zai amfani Al'ummar Musulmi, ka zama farkon wanda zai taimakawa wannan da zai yi alherin ka zama kuma mai Ζarfafar guiwa, kar kazo kana Sharri.
Ita Da'awah ta Musulunci, tazo ne don ta karantar da Musulmi su zama masu tausasawa da kyautatawa tare da duk wani wanda ya tayar da wani alheri, kada wannan mai Da’awa na Musulunci ya taΖaitu da cewa sai abunda shi ya fara shine alheri, don haka duk abunda bashi ya fara ba, ba alheri bane❗️.
π ANNASIHA TV
