HATTARA DAI Ζ³AN MATA! π©π½π¦³
Zan yi amfani da wannan damar ne domin fadakar da Ζ΄an uwana Musulmi musamman (Ζ³anmata da Samari) akan wata Ιabi'a da yanzu ta zama ruwan dare a cikin mu.
.
*IDAN KI NA SO NA, KI NUNA MIN;*
.
Wannan zance ne da mafi yawancin samari a yau su ke amfani da shi domin cin ma manufarsu akan budurwa musamman idan suka lura cewa Ta kamu da son su. Su na yin haka ne domin samun damar taΙa jikin budurwa, ko yin kissing Ιinta ko rungumarta da sunan wai nuna Soyayya, wanda yin hakan wani kofa ce da kusantar Zina, wanda kuma Allah Ya yi hani ga kusantar zina.
.
Ya ke Ζ³ar uwa! Kada ki yarda Gaye ya yi maki wasa da hankali, Ke fa ba Ζaramar yarinya ba ce, Ki yi tunani! Duk namijin da ze neme ki da ki yi Kissing ko Hugging Ιinsa ba tsakani da Allah ya ke son ki ba. Domin saurayi na Ζwarai, shi ne wanda a koda yaushe ya ke da burin kare martabar Masoyiyarsa.
.
Ki sani! Addinin musulunci ya kare maki martabarki, to don me za ki bama wani Ζazami damar zubar maki da ita.
.
Ka da Ki yarda wani Namiji ya samu damar taΙa jikinki ballantana ya rungumeki ko Kissing Ιinki.
.
Ya kai Ζan uwa! Ka ji tsoron Allah, Menene ribar ka don ka taΙa jikin macen da ba taka ba, Ka sani,
.
An karbo daga MaΖil bn Yassaar (r.a) ya ce: Manzon Allah ο·Ί ya ce: *“Da Ιayanku ya taΙa matar da bata halasta a gareshi ba, gara an soka mashi allura ta Ζarfe a kansa”* Ζabaraani ya ruwaito shi, a al-kabeer 489. Albani ya inganta hadisin.
.
Wannan hadisin na nuna mana cewa Azabar namiji mai taΙa mace, ko macen da ke taΙa Namijin da ba muharraminta ba ya fi a daΙa ma mutum allura a kanshi, saboda haka Wallahi mu ji tsoron Allah domin yana kallonmu a duk inda muke.
.
Kuma haramunne yin hannu tsakanin Namiji da Mace matuΖar ba Muharraman juna bane, hadisi ya tabbata daga Annabi (ο·Ί) cewa ya ce: *“Ni ba na yin hannu da mata....”* har zuwa Ζarshen hadisin, Kuma Allah (ο·») Ya ce: “HaΖiΖa abin koyi kyakkyawa ya kasance a gareku wajen manzon Allah” Don haka dole ne a kan mu kada mu yi hannu da mata, domin koyi da Annabi (ο·Ί).
.
Ya Ζ³an uwana Musulmi, Ni ina yi maku nasiha akan ku Nisanci duk wani abu da ze kai ku ga fushin Ubangiji.
.
Ya ke Ζ³ar uwata mai daraja ka da ki yarda ku keΙance da saurayi ko wani namiji ba tare da wani muharramin ki a wajenba, domin Annabi (ο·Ί) ya ce: *“Wanda ya kasance yana Imani da Allah da Ranar lahira, to kada ya kuskura ya kaΙaita da mace ba tare da muharraminta na tare da ita ba, domin na ukunsu shi ne ShaiΙan”*
.
Daga Ζarshe, Ya ku Ζ³an uwana Muminai Maza da Mata! Ina tunatar da ku Wasiyyar Allah a gareku a inda yake cewa:
.
*“Ka ce da muminai maza su kame ganinsu, kuma su kiyaye farjinsu. Wannan shi ya fi tsarki a gare su. HaΖiΖa Allah Masanin abin da su ke aikatawa ne. Ka ce da muminai mata su kame ganinsu, kuma su kiyaye farjinsu. Kada kuma su fito da adonsu, saidai abinda ya bayyana daga gare shi, kuma su yi lulluΙi da mayafansu a kan wuyan rigunansu. Kuma kada su bayyana adonsu sai ga mazajensu, ko Ζ΄aΖ΄ayensu, ko Ζ΄aΖ΄ayen mazajensu, ko Ζ΄an uwansu maza, ko Ζ΄aΖ΄an Ζ΄an uwansu maza, ko Ζ΄aΖ΄an Ζ΄an uwansu mata, ko mata (musulmai) Ζ΄an uwansu, ko kuma abinda hannayensu suka mallaka (bayi), ko kuma mabiya ba masu bukatar mata ba daga maza, ko kuma Ζananan yara waΙanda basu san sha'awar al'aurar mata ba. Ka da kuma su buga Ζafafunsu don a gane abin da suka Ιoye na adon Ζafafunsu (wato mundaye). Kuma ku tuba ga Allah gaba Ιayanku ya ku waΙannan muminai don ku rabauta”*. (An-Nur: 30, 31)
.
Anan ne zan dakata da rubutu Na, Allah Ya shiryar damu a hanya madaidaiciya.
.
*Ayyub Musa Jebi.*
*08166650256.*
*26/01/2018.*
*πIrshadul Ummah WhatsApp.*
