MA’ANAR MUTU’A: AUREN WUCIN GADI

MA’ANAR MUTU’A:  AUREN WUCIN GADI 


Mutu’a, ko kuma auren wucin gadi, watau auren da ba na dun-dun- dun ba, ma’anarsa shi ne namiji ya Ζ™ulla jinga da mace cewa zai sadu da ita sau Ι—aya ko sau biyu, ko kuma na tsawon awa Ι—aya, ko kwana kaza, ko wata kaza, a kan kuΙ—i kaza ko ladan abu kaza.  

Auren Mutu’a yana cikin aurace-auracen Jahiliya kuma an yi aiki da shi a farkon Musulunci kana daga bisani aka haramta shi.  An karΙ“o ruwaya daga Ali binu Abi Ɗalib (R.A), cewa “Manzon Allah (SAW) ya hana auren Mutu’a da cin naman jakin gida a lokacin (yaΖ™in) Khaibar.” *[Bukhari da Muslim].*

Amma Ζ΄an Shi’a sun ci gaba da halasta Mutu’a kuma sun Ζ™ago ruwayoyin Ζ™arya waΙ—anda suka nuna falalarta da Ι—umbin ladan wanda ya yi ta, da kuma darajarsa a aljanna. Babu shakka sun yi haka domin su Ι“ata al’ummar Musulmi ta hanyar yaΙ—a lalata da Ι“arna da alfasha a tsakaninsu kuma don su jawo hankalin jahilai, musamman matasa, zuwa ga tafarkinsu.  
 
*Falalar Mutu’a:*
Akwai Ι—aruruwan ruwayoyi a cikin littafan malaman Shi’a da suke izna da su waΙ—anda suke nuna falalar auren wucin gadi.  Ya zo a cikin littafin *Man La Yahduruhul FaΖ™ih*, Ι—aya daga cikin littafansu guda huΙ—u mafiya inganci, sun laΖ™a ma Ja’afar SadiΖ™, Imaminsu na shida, cewa ya ce: “Lallai Mutu’a addinina ce kuma addinin iyayena. Wanda ya yi aiki da ita ya yi aiki da addininmu kuma wanda ya yi inkarin ta ya yi inkarin addininmu, kuma ya yi riΖ™o da wanin addininmu.” [ *Ibnu Babawaih Alkummi, Man La Yahduruhul Fakih, bugun Darut Ta’aruf, Bairut, 1401 B.H., mujalladi na 3 shafi na 336].* 
Ya zo a wannan littafi har yau, sun dangana ga Annabi (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya yi Mutu’a sau Ι—aya zai amince fushin Allah, wanda ya yi Mutu’a sau biyu za’a tashe shi tare da zaΙ“aΙ“Ι“un bayi, wanda ya yi Mutu’a sau uku zai haΙ—a kafaΙ—a da ni a aljanna.” *[A duba Man La Yahduruhul Fakih na Alkummi, muj. na 3 sha. 336]* . A wata ruwayar mai kama da wannan, sun Ζ™aga wa Manzon Allah (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya yi Mutu’a sau Ι—aya za ta zama (gare shi) kamar darajar Hussaini (A.S); wanda ya yi Mutu’a sau biyu darajarsa kamar darajar Hassan (A.S) ce; wanda ya yi Mutu’a sau uku darajarsa za ta kasance kamar darajar Ali (A.S); kuma wanda ya yi Mutu’a sau huΙ—u darajarsa kamar darajata ce.” *[Fatahallah Kashani, Tafsiru Minhajis Sadikin, bugun Maktabatus Sadar, Tehran-Iran, 1379 B.H., muj. na 2 sha. na 493]* .

Da yake mata suna da Ζ™arin kunya a kan maza, wataΖ™ila za su buΖ™aci a Ζ™ara Ι—an ingiza su kaΙ—an kafin su faΙ—a ramin alfasha. Don haka AlΖ™ummi, wanda suke yi wa laΖ™abi da AlsaduΖ™ (watau mai yawan gaskiya!) ya kitsa musu tasu ruwaya ta musamman. Ya ce, “Lokacin da aka yi isra’i da Annabi (SAW) zuwa sama, ya ce: Jibrilu ya riske ni ya ce:  Ya Muhammad, Allah mai girma da Ι—aukaka yana cewa: Lallai ni na gafartawa masu yin Mutu’a daga matayen al’ummarka.” *[A duba Man La Yahduruhul Fakih, muj. na 3 shafi na 463].*   
 
*Ladan Mai Yin Mutu’a:*  
Abinda ya gabata dangane da falala da Ι—aukakar darajar mai yin auren Mutu’a ne. Amma dangane da Ι—umbin ladan da zai samu, bari mu saurari AlsaduΖ™ ya Ζ™ara shara mana ita. Ya ce:  an tambayi Abu Abdullahi, watau Imamin Shi’a na shida:  Shin mai yin Mutu’a yana da lada?  Sai ya ce, “In yana nufin yardar Allah da ita (Mutu’ar) ba zai yi magana da ita ba (matar) kalma guda face Allah ya rubuta masa lada da ita (kalmar), kuma idan ya kusance ta sai Allah ya gafartar masa zunubi, kuma idan ya yi wanka Allah zai gafarta masa da gwargwadon ruwan da ya shuΙ—e a kan gashinsa.” *[Man La Yahduruhul Fakih, muj. na 3 sha. na 336].*    
*GargaΙ—i ga Wanda Ya Ƙi Yin Mutu’a* 

Bayan bayanin falala da garaΙ“asar Mutu’a, idan da akwai wani mai taurin kai wanda ya Ζ™i Ι—ibar wannan garaΙ“asa, to sai a yi masa gargaΙ—i kuma a tsoratar da shi. Wannan shi ne abinda malamin Shi’a, mai suna Alfailul Kashani, ya yi a yayin da ya ruwaito daga Annabi (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya fita daga duniya bai yi Mutu’a ba, zai zo ranar AlΖ™iyama yana yankakke (watau naΖ™isin halitta).” [ *A duba Minhajus Sadikin na Kashani, mujalladi. na 2 shafi. na 489].*

A harshen Shari’a, irin wannan gargaΙ—i ana yin sa ne ga wanda ya aikata kaba’ira, watau babban zunubi, kamar shaidar zur, ko gudu daga fagen fama, ko saΙ“a wa iyaye da sauransu.  

Saboda haka za mu fahimta a nan cewa, Ζ™in yin Mutu’a dai-dai yake da aikata kaba’ira. Kuma wannan babu mamaki idan muka dubi waccan ruwaya da ta gabata wacce take cewa, “Wanda ya yi inkarinta ya yi inkarin addininmu.”  

Wannan ya sa Sayyid Hussain Almusawi, wanda a da Ι—an Shi’a ne kuma Allah ya shirye shi ya tuba, yake cewa manyan malaman Shi’a na wannan zamani, kamar su Sayyid Assadar da Alburujardi da Asshirazi da AlΖ™azwini da AlΙ—ibaΙ—iba’i da Abu Harith Alyasiri da kuma uban tafiya, Imam Khumaini, duka suna yin Mutu’a, kuma suna yin ta da yawa ba kaΙ—an ba! [ *Sayyid Hussain Musawi, Kashful Asrari wa Tabri’atil A’immatil Adhari, bugun Darul Iman, Alkahira, 2002, sha. na 34-35].*      

A bisa mafi rinjayen zato, Rafilawan Nijeriya ma suna yin mutu’a, kuma Mutu’a na cikin hanyoyin yaudara da suke jawo hankalin jahilai da su, musamman matasa maza da mata, zuwa ga wannan tafarki nasu mai nufin rushe durakun al’umma. 



*- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 4: "Auren Mutu’a a wajen Ζ³an Shi’a" - na Prof. Umar LabΙ—o*

*✍ AnnasihaTv*

 ```- Ga masu son siyen littafan da ma wasu littafan Prof sai su tuntuΙ“e mu kamar haka``` ;

*Call/WhatsApp:* 08142286718

*Twitter*: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09
Post a Comment (0)