MA’ANAR MUTU’A: AUREN WUCIN GADI
Mutu’a, ko kuma auren wucin gadi, watau auren da ba na dun-dun- dun ba, ma’anarsa shi ne namiji ya Ζulla jinga da mace cewa zai sadu da ita sau Ιaya ko sau biyu, ko kuma na tsawon awa Ιaya, ko kwana kaza, ko wata kaza, a kan kuΙi kaza ko ladan abu kaza.
Auren Mutu’a yana cikin aurace-auracen Jahiliya kuma an yi aiki da shi a farkon Musulunci kana daga bisani aka haramta shi. An karΙo ruwaya daga Ali binu Abi Ζalib (R.A), cewa “Manzon Allah (SAW) ya hana auren Mutu’a da cin naman jakin gida a lokacin (yaΖin) Khaibar.” *[Bukhari da Muslim].*
Amma Ζ΄an Shi’a sun ci gaba da halasta Mutu’a kuma sun Ζago ruwayoyin Ζarya waΙanda suka nuna falalarta da Ιumbin ladan wanda ya yi ta, da kuma darajarsa a aljanna. Babu shakka sun yi haka domin su Ιata al’ummar Musulmi ta hanyar yaΙa lalata da Ιarna da alfasha a tsakaninsu kuma don su jawo hankalin jahilai, musamman matasa, zuwa ga tafarkinsu.
*Falalar Mutu’a:*
Akwai Ιaruruwan ruwayoyi a cikin littafan malaman Shi’a da suke izna da su waΙanda suke nuna falalar auren wucin gadi. Ya zo a cikin littafin *Man La Yahduruhul FaΖih*, Ιaya daga cikin littafansu guda huΙu mafiya inganci, sun laΖa ma Ja’afar SadiΖ, Imaminsu na shida, cewa ya ce: “Lallai Mutu’a addinina ce kuma addinin iyayena. Wanda ya yi aiki da ita ya yi aiki da addininmu kuma wanda ya yi inkarin ta ya yi inkarin addininmu, kuma ya yi riΖo da wanin addininmu.” [ *Ibnu Babawaih Alkummi, Man La Yahduruhul Fakih, bugun Darut Ta’aruf, Bairut, 1401 B.H., mujalladi na 3 shafi na 336].*
Ya zo a wannan littafi har yau, sun dangana ga Annabi (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya yi Mutu’a sau Ιaya zai amince fushin Allah, wanda ya yi Mutu’a sau biyu za’a tashe shi tare da zaΙaΙΙun bayi, wanda ya yi Mutu’a sau uku zai haΙa kafaΙa da ni a aljanna.” *[A duba Man La Yahduruhul Fakih na Alkummi, muj. na 3 sha. 336]* . A wata ruwayar mai kama da wannan, sun Ζaga wa Manzon Allah (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya yi Mutu’a sau Ιaya za ta zama (gare shi) kamar darajar Hussaini (A.S); wanda ya yi Mutu’a sau biyu darajarsa kamar darajar Hassan (A.S) ce; wanda ya yi Mutu’a sau uku darajarsa za ta kasance kamar darajar Ali (A.S); kuma wanda ya yi Mutu’a sau huΙu darajarsa kamar darajata ce.” *[Fatahallah Kashani, Tafsiru Minhajis Sadikin, bugun Maktabatus Sadar, Tehran-Iran, 1379 B.H., muj. na 2 sha. na 493]* .
Da yake mata suna da Ζarin kunya a kan maza, wataΖila za su buΖaci a Ζara Ιan ingiza su kaΙan kafin su faΙa ramin alfasha. Don haka AlΖummi, wanda suke yi wa laΖabi da AlsaduΖ (watau mai yawan gaskiya!) ya kitsa musu tasu ruwaya ta musamman. Ya ce, “Lokacin da aka yi isra’i da Annabi (SAW) zuwa sama, ya ce: Jibrilu ya riske ni ya ce: Ya Muhammad, Allah mai girma da Ιaukaka yana cewa: Lallai ni na gafartawa masu yin Mutu’a daga matayen al’ummarka.” *[A duba Man La Yahduruhul Fakih, muj. na 3 shafi na 463].*
*Ladan Mai Yin Mutu’a:*
Abinda ya gabata dangane da falala da Ιaukakar darajar mai yin auren Mutu’a ne. Amma dangane da Ιumbin ladan da zai samu, bari mu saurari AlsaduΖ ya Ζara shara mana ita. Ya ce: an tambayi Abu Abdullahi, watau Imamin Shi’a na shida: Shin mai yin Mutu’a yana da lada? Sai ya ce, “In yana nufin yardar Allah da ita (Mutu’ar) ba zai yi magana da ita ba (matar) kalma guda face Allah ya rubuta masa lada da ita (kalmar), kuma idan ya kusance ta sai Allah ya gafartar masa zunubi, kuma idan ya yi wanka Allah zai gafarta masa da gwargwadon ruwan da ya shuΙe a kan gashinsa.” *[Man La Yahduruhul Fakih, muj. na 3 sha. na 336].*
*GargaΙi ga Wanda Ya Ζi Yin Mutu’a*
Bayan bayanin falala da garaΙasar Mutu’a, idan da akwai wani mai taurin kai wanda ya Ζi Ιibar wannan garaΙasa, to sai a yi masa gargaΙi kuma a tsoratar da shi. Wannan shi ne abinda malamin Shi’a, mai suna Alfailul Kashani, ya yi a yayin da ya ruwaito daga Annabi (SAW) cewa wai ya ce: “Wanda ya fita daga duniya bai yi Mutu’a ba, zai zo ranar AlΖiyama yana yankakke (watau naΖisin halitta).” [ *A duba Minhajus Sadikin na Kashani, mujalladi. na 2 shafi. na 489].*
A harshen Shari’a, irin wannan gargaΙi ana yin sa ne ga wanda ya aikata kaba’ira, watau babban zunubi, kamar shaidar zur, ko gudu daga fagen fama, ko saΙa wa iyaye da sauransu.
Saboda haka za mu fahimta a nan cewa, Ζin yin Mutu’a dai-dai yake da aikata kaba’ira. Kuma wannan babu mamaki idan muka dubi waccan ruwaya da ta gabata wacce take cewa, “Wanda ya yi inkarinta ya yi inkarin addininmu.”
Wannan ya sa Sayyid Hussain Almusawi, wanda a da Ιan Shi’a ne kuma Allah ya shirye shi ya tuba, yake cewa manyan malaman Shi’a na wannan zamani, kamar su Sayyid Assadar da Alburujardi da Asshirazi da AlΖazwini da AlΙibaΙiba’i da Abu Harith Alyasiri da kuma uban tafiya, Imam Khumaini, duka suna yin Mutu’a, kuma suna yin ta da yawa ba kaΙan ba! [ *Sayyid Hussain Musawi, Kashful Asrari wa Tabri’atil A’immatil Adhari, bugun Darul Iman, Alkahira, 2002, sha. na 34-35].*
A bisa mafi rinjayen zato, Rafilawan Nijeriya ma suna yin mutu’a, kuma Mutu’a na cikin hanyoyin yaudara da suke jawo hankalin jahilai da su, musamman matasa maza da mata, zuwa ga wannan tafarki nasu mai nufin rushe durakun al’umma.
*- JERIN LITTAFAN SHI’A NA 4: "Auren Mutu’a a wajen Ζ³an Shi’a" - na Prof. Umar LabΙo*
*✍ AnnasihaTv*
```- Ga masu son siyen littafan da ma wasu littafan Prof sai su tuntuΙe mu kamar haka``` ;
*Call/WhatsApp:* 08142286718
*Twitter*: https://twitter.com/AnnasihaTv?s=09
