DAN ACHABA ZAI IYA KAI KIRISTA COCI?

DAN ACABA ZAI IYA KAI KIRISTA COCI?

Tambaya:

Assalamu alaikum, Akramakallahu, Shin ya halatta MUSULMI DAN ACABA ya dauki KIRISTA ya kai Shi COCI, ko ya dauko Shi daga Coci zuwa gida? Domin Suna cewa: Mu Sana'a kawai Mu ke yi, haka abin ya ke a bangaren MAGINA, TELOLI, KAFINTOCI da MA SU WAYARIN da sauran su.

Amsa:

To dan uwa Allah Madaukakin Sarki Ya hana taimakekeniya wajan aikata sabo, kamar yadda aya ta biyu a suratul Ma'ida ta tabbatar da hakan.

Yana daga cikin sharuddan cinikayya ya zama ta hanyar da shari'a ta yarda, wannan ya sa kafinta da magini ba za su taimaka wajan gina inda za a saba wa Allah ba, ko da kuwa za su samu kudi, kamar yadda bai halatta Tela ya dinka kayan da za a  sanya a coci a kira wanda ba Allah ba.

Duk wanda ya wadatu Allah Zai wadatar da shi, wanda ya kame Allah Zai kamar da shi, Wadatar zuci taska ce da bata karewa.

Don neman Karin bayani duba: Al'umm 4\213. Da kuma Iktidha'u siradil mustakim 2\41.

Allah ne mafi Sani

Amsawa:
Dr Jamilu Yusuf Zarewa
12\2\2016.

Daga: ZAUREN FIQHUS SUNNAH

Post a Comment (0)