MAIRO 03

♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*3*

tafe Mairo take ɗauke da turenta na giɗa saman kai tana yan wakewakenta.
saida tayi nisa da tafiya sannan ta tuno da ɓanɓaramar da tayi jiya da sauri ta chaja hanya harda haɗawa da ɗan gudu tana waigen bayanta.
saida taga ta shanye kwana sannan hankalinta ya kwanta tafiya ta rik'ayi a hankali tana kwanɗalar giɗar tana ci.

kashe kunne tayi tayi gefen dashi tana son ta tabbatarda abunda kunnuwanta suke jiyo mata.
wak'ar india ce _ghajiniguzarish_ ke tashi cikin wani kiɗan taushi mai daɗi
taɓe baki tayi "tho wai wayasa wannan kiɗan mai ɗaɗi cikin ɗaji kodai buki ake?" magana take tana kallon giɗar dake hannunta kamar wata taɓaɓɓiya.
kara kasa kunne tayi har ta gano gefen da sautin ke tashi dariya tayi "Allah buki ne ake bari na leka na gani amman ba zan daɗe ba sai na dawo"
haka ta kunna kai daga wani ɓangare na hanyar ta rika tafiya tana bin inda taji sautin wakar na tashi harta iso wani guri mai kamada lambu.
tsayawa tayi tana kallon etacen dake gurin "lahhh ashe ma haka gurin yake ni kan ban taba zuwa ba sai yau"
rabon ido ta shigayi saida ta kare kallon gurin sannan ta cigaba da tafiya.
a hankali ta fara hango wasu mutane sanye da wani yadi kala ɗaya.
da sauri ta laɓe gefen ecce tana lekensu ,

duk kansu sanye suke da yadi kala ɗaya mai ja da kore (red and green) kana gani kasan fadawa ne in banda mutun biu dake zaune saman wani k'aton carpet na alfarma ɗayan sanye yake da riga da waddo na turawa ɗayan kuma sanye yake da riga doguwa mai kamada jalabiyar fakistan _golden color_ Mai kyau sai kyali take.
ya dora wani ɗan kyale saman wuyansa daya sauko har saman rigarsa.
gashin kansa ya kwanta lum kamar balarabe ya lankwashe kafafunsa wata rekoda na gefensa tana bada sauti shi kuma yana fuskarta ɗayan suna karta ko wannensu kuɗi yake azawa in aka cinye ya kara wasu.

        sosai abunda suke ya burge Mairo aje turen giɗar tayi tayi zaune tana kallonsu tana dariya amman baki rufe dan kar suji
ta daɗe a haka can dai taji bazata iya jurewa ba ta ɗauki turenta ta nufosu tana Murmushi.
"Assalamu alaikum"
sallama tayi musu tana k'ok'arin k'arisawa kusa dasu
   da sauri suka tare wadda ke zaune saman carpet ɗin wasu kuma suka nufota rik'e da takobi.
tsaye tayi tana kallonsu kamar hoto har suka karaso kusa da ita,
wani zarare cikinsu ya ɗaga takobi zai sara mata ɗayan yayi saurin  rikewa yana faɗin "Yarima yace a dakata"
da sauri ya janye takobin yayi baya.
ɗaya daga cikin fadawan ya fisgota da karfi har giɗar dake saman kanta ta watse ya nufi gurin yarima da ita.
yana tsaye yana kallonsu har suka iso da ita kallo ɗaya yayi mata ya gane bata cikin hayyacinta ganin yadda idonta suka k'afe kuma bata motsi.
    ido ya ɗan tsura mata sannan ya bada umarnin a zuba mata ruwa,

da sauri bafaden ya dauki ruwan gora ya watsa mata
sai a lokacin ta matsa alamar ta dawo hayyacinta zubewa tayi zaune ta ɗaga kai tana kallonsu
suma ita suke kallo har yarima saida ta kare kallonsu ɗaya bayan ɗaya sannan ta saki wata irin kara iya karfinta mai shiga cikin kwakwalwa faɗuwa yarima yayi zaune ya dafe kunnunwansa shida wadda ke kusa dashi.
mari daya daga cikin fadawan ya watsa mata saida ta faɗi can gefe ta fashe da kuka
     ɗagowa yarima yayi ya watsa masa wata mugunyar harara da sauri bafaden ya faɗi kasa "Allah ya huci zuciyarka Yarima banyi dan ranka ya bace ba"
kawarda kai yayi yana sauraren sautin kukanta dake tashi tare da sautin waka

ya daɗe a haka sannan ya ɗago cike da isa yace "kashe sautin nan" da sauri ya tashi ya nufi rikodar sa hannu ya kashe ya dawo ya risina gaban Yarima yana faɗin "Allah karawa Yarima martaba na kashe"
ba tare daya kalleshi ba yace
"jeki ka rarrasheta"
"am gama Yarima" tashi yayi da sauri ya nufi gurin Mairo.

tirgewa Mairo ta karayi tana kuka tana kiran gwaggo tana murza hannayenta da kafafunta cikin kasa,
yayita rarrashinta har ya gaji tak'i tayi shiru sai ma karawa take.
ganin tak'iyin shiru yasa Yarima yayi mata alamar tazo da hannun tashi tayi ta share hawayenta ta nufoshi tana murmushi kamar ba ita ba.
kallonta yake harta karaso kusa dashi tun kamin yayi mata magana ta zauna saman carpet ɗin kusa dashi.
       da sauri ɗaya daga cikin bafaden ya unkuro zai mata magana Yarima ya ɗaga masa hannu nan dukansu suka ja baya kowa ya shiga harkar gabansa.
kallonta yayi a natse cikin isa yace

"ya sunanki?"
washe masa hauru tayi
"Mairo"

"Mairo?"

"eh sunana Maryam amman Mairo ake cemin kaifa ya sunaka?"

bai amsa mata ba ya jefa mata wata tambayar "an garin kike?"
"eh kai amman dai ɗan birni ne ko?"
nan ma wata tambayar ya sake jefa mata batare daya amsa mata ba
"mi kikazo yi nan?"
"talla nake zan wuce sai naji kiɗi na ɗauka bukine ake shine nace bari nazo na gani saina koma shine na ganku sai na taɓe"
shiru ya ɗanyi yaɓa kallonta sannan yace
"tho miyasa kika fito?"
abunda ke gabansa ta ɗauka ta nuna masa "wasan da kuoe da wannan abun ya burgeni shiyasa na fito"
bai sake ce mata komai ba ya janyo wayarsa ya shiga danne2

sai a lokacin Mairo ta tuno da giɗarta
hannu ta ɗora saman kai ta fasa kuka
"wayyo na shiga uku giɗata"
wani mugun tsaki wadda ke kusa da Yarinan yaja yana hararta.
a hankali Yarima ya ɗago kai ya kalleta
"ina giɗar take?"
"nima ban saniba ɗazu dai kamin nayi bachi nasan tana saman kaina"
kallon rashin fahimta yayi mata "bachi kikayi?"
"eh ɗazu da suka nufoni da takobi ba sai naji bachi dana farka sai naganni nan kuma banga giɗar ba"
murmushi yayi dan ya gane suma take nufi da bachi.
ɗaya daga cikin fadawansa ya kira da sauri yazo gabansa ya risina cikin isa Yarima yace
"ina giɗar Yarinyar nan?"
"gata can kusa da ecce ta zubar"
"jeki ka ɗauko mata"
tashi yayi da sauri ya nufi gurin yana faɗin "am gama Yarima"
kallon Yarima tayi tana dariya "na gode"
kai kawai ya ɗaga mata
ta sakar masa murmushi tace
"kai baka fada min sunanka ba?"
yi yayi kamar bai jita ba ya mai yarda idonsa wani gefen
nan mairo ta ɓata fuska ta buro baki
"ni inna tambayeka saika kyaleni nima amsar da na baka ban yafe ba lafira saika biyani"
cikiciki take maganar amman hakan bai hanashi ji ba
dariya ce tazo masa da sauri ya mayarda ita murmushi ya kara kawarda fuskarsa.

*© Khadeeja Candy*

Post a Comment (0)