MAIRO 04

♡... MAIRO ...♡*

*BY*
 
    *_KHADEEJA CANDY_*

*4*

suna haka nafaden ya kawo mata turen giɗarta ya aje yana faɗin "gashi Yarima Allah ya kara maka daraja"
hannu ya ɗaga masa bafaɗen ya tashi.
kallonsa Mairo tayi "na gode"
banza yayi mata kamar bai jita ba sun daɗe a haka sannan ya juya ya kalleta yace "amsar da kika bani zan biyaki lahira?"
shru tayi tana kallonshi dan batayi zaton yaji ba can tace "eh mana tunda kai baka banu amsar tambaya ta ba"
shiru ya ɗanyi sannan yace "mi kike tambayeni?"
"ba nace ka faɗa min sunanka ba"
ya ɗan daɗe kamin ya bata amsa "sunana Yusuf Usaini"
dariya tayi harda sa hannun baki "lahhhh shiyasa kake da kyau daman masu suna Yusuf suna da kyau"
murmusawa ya ɗanyi ya ɗauki enabi yakai bakinshi.
yatsa ɗaya Mairo ta ɗaga masa "sauran tambaya ɗaya" 
kai ya ɗaga mata yana tsusar enabi kamar mai shan minti.
tsaki kawai na kusa dashi keja haushi ya isheshi
harara Mairo ta watsa masa ta kalli Yarima tace "amman dai ɗan bunni ne ko?"
murmushin gefe yayi ya ɗaga mata kai alamar 'eh' waje tayo da ido ta shiga shafa mishi riga "lahhh nikan daman nace dan bunni ne kai inason yan bunni kuma..."
"ke! mahaukaciya"
bata karasa maganar ba na kusa dashi ya katsa mata tsawa saida ta razana
hmda sauri Yarima ya ɗaga mishi hannu yana kallon fuskar Mairo data k'ara rik'e masa riga tana kallon mutunen.
tsaki ya k'ara ja ya kalli Yarima "haba Yarima ya zaka..."
dakatar dashi Yarima yayi ba tare daya kalleshi ba yace "enough yahuza plz excuse us"
tashi yayi cike da bachin rai ya nufi wta bishiya ya zauna.

sai lokacin Mairo ta turo baki tayi kwafa "tho an taɓa shi zo kayi abunda zakayi mai k'aton kai"
murmushi Yarima yayi yace "baki tsoron ya dakeki?"
kai ta kaɗa "ni wlh bana tsoron duka nifa ko sheɗan bai kaini masifa ba"
faɗaɗa murmushinsa yayi "gaskiya ne tho tashi zaune"
tashi tayi zaune ta ɗauki ruwan dake gansa "insha ruwan bunni?"
kai ya ɗaga mata yana kakkaɓe rigarsa data bata da k'asar hannunta.
saida ta shanye ruwan kofin gaba ɗaya sannan ta dire kofin tana dariya tana faɗin "wlh na sha ruwan bunni"
"birni ake cewa ba bunni ba"
ya gyara mata
washe hakora tayi ta sake cewa "bunni"
murmushi yayi yace "waya shafa miki hoda?"
"nice na shafa ɗazu da zanje tallah"
ta karasa maganar tana gyaran ɗankwalinta.

can ta ɗauki abunda ke gabanshi ta kalleshi tace "minene kuke da wannan abun ɗazu naga kuna wasa dashi?"
saida ya ɗan daɗe sannan yace "chachace muke zakiyi?"
da sauri ta matso kisa dashi tace "eh zanyi dan Allah"
"tho mi zaki aza?"
"kamar ya mi ake azawa"
"duk abun mutum kr so yana azawa bakiga yadda muke yi ba ni kuɗi nake azawa"
kalle2 ta shigayi tana neman abunda zata aza can ta kalli giɗar ta da sauri ta ɗauko k'waya ɗaya ta aza "to ga giɗa nan na aza"
shafa kansa yayi yayi murmushi ya sa hannunsa aljihu ya ciro dalar amerika ɗaya ya aza.
bata fuska Mairo tayi ta turo baki "ni dai bana son wannan takardar da kuke da ita saida ka aza kuɗi ko wani abu mai daɗi"
ta karasa maganar tana lek'en lemun dake bayansa.
ido ya tsura mata yana mamakin wayonta wato shi ya aza (ɗora) kudin data sani ko abu mai daɗi ita kuma ta aza kwaya ɗaya ta giɗa
cikiciki yayi murmushi yace "ai kuɗi ne ba takarda bace in kika chaja kuɗi da yawa za a baki"
lak'e kafaɗa tayi "ban yarda ba kuɗi bane ai da na sansu saidai ka aza kuɗin k'warai"
"ba nida wayan can kuɗin da kika sani wannan ne kawai in kuma ba zakiyi ba shi kenan"
shiru tayi tana son masa musu shima shirun yayi yana kallonta.
da taga babu sarki sai Allah yasa ta kalleshi tace "na amince"
kai ya kaɗa mata ya ɗan daɗe sannan ya gyara zamansa suka fara.
yin kawai suke tana masa shirme dan bata iyaba ci kusan 10 yayi mata sai haushi take ji dak'er ta samu tayi masa ci biu koshi danya nuna mata yadda zatayi ne.
aiko murna kamar ta kasheta sai dariya take kwasa harda hawaye.
shidai kallonta kawai yana shakkun hankalinta.

da taga ya kara mata ci biu ta ɓata fuska tace
"nidai na daina kuma saika bana giɗata"
shiru yayi yana kallonta kamar ba zaiyi magana ba saida yaga ta fara turo masa baki sannan yace
"ni kuma kuɗina dana baki fa?"
ɗaukar kuɗin tayi ta kikkiresu tayi musu guntu guntu baiyi unkurin hanata ba saida ta k'are  ta watsar  ta kalleshi tace "ni bana sonsu"
"mi yasa kikayi haka bakisan ba kyau yaga kuɗi ba?"
"ai ba kuɗi bane takardace nidai bani giɗata"
banza yayi mata ya ɗauke kansa saida yagata soma yi masa kuka sannan ya ɗauki giɗar ya mik'a mata ta da sauri ta karɓa tasa a ture ta tashi ta karkaɗe jikinta ta ɗora turan saman kai tayi masa murmushi ta kama hanya.

har tayi nisa sai kuma tayi juyo ta nufoshi.
kaɗan kaɗan take tafiya tana turo baki har ta karaso kusa dashi ta sauke turen ta aje masa ta fashe da kuka.
kallon kawai yake tun tana kuka ba hawaye harta fara hawayen tana shureshuren kafafunta cikin k'asa sai kallonshi take,
shima ita yaƙke kallo yana tsusar baki kamar mai mai shan minti.
sunfi karfin minti 30 a haka ita taki tayi maganar sai kuka take shina yaki yayi mata magana fadawansa sai satar kallonsu suke yahuza ko yasa earphone a kunne dan kar haushi ya kasheshi.

saida yaji ta kara buɗe baki tana kiran Gwaggo sannan ya matsa ya rik'o fuskarta ya sakar mata manya idonsa yace "mi kike yiwa kuka?"
cikin kukan tace "ba kaine ba ka jani da wasa har lokacin komawa gida yayi ban siyar da giɗa ba kuma Gwaggo bazata bani kuɗin sawa asusu ba"
murmushi yayi yasa wani bafaden sa ya kira masa yahuza.
haka ya iso gurin yana hararar Mairo.
Yarima ya kalleshi yace "kuɗin nageriya nake so"
hannu yasa aljihu ya ciro yan dubu dubu ya aje masa gabansa.
nan ne yaga kuɗin da Mairo ta yaga kallon Yarima yayi yace "wayayi wannan aikin?"
kallon Mairo Yarima yayi bai bashi amsa ba hakan ya tabbatar masa da itace 'uhmmm' kawai yace ya watsa mata harara ya koma gurin zamansa.

Yarima ya kalli Mairo yace "ɗauki ko nawa kike so"
da sauri tasa hannu ta dauki dubu uku tana dariya tace "na gode"
kai ya ɗaga mata "sun isheki?"
"eh na gode amman dan Allah ka bani wacan abun"
juyawa yayi yana kallon apple ɗin data nuna masa.
hannu yakai ya dauki ɗaya ya mika mata tana karɓa takai baki "lahhh daman haka goribar bunni take?"
murmushin gefe yayi ya girgiza mata kai "ba goriba bace apple ne"
"minene apple?"
"tuffa"
"minene tufa?"
shiru yayi dan yanzu kam baisan mi zai ce mata ba.
kamin yayi mata wata magana ta sake rokonsa
"dan Allah karamin ɗaya na kaiwa Gwaggo"
kara ɗauko ɗaya yayi ya mika mata dariya tayi ta kara rok'onsa "na gode amman ɗan Allah kara min ɗaya na kaiwa k'awata jummalo (MANIRA Lol.) da Halilu hannu yasa ya sake ɗaukowa ya mika mata.
bata bar gurin ba saida ta lisafa masa mutum takwas ya bata sannan ta tashi ta ɗora ture tana dariya tayi masa godiya tare da sallama ta nufi hanyar fita gurin tana waigensa tana ɗago masa hannu shidai kallo kawai ya bita dashi da murmushi harta fice.

© *Khadeeja Candy*

Post a Comment (0)