TUN KAFIN AURE 46

TUN KAFIN AURE💐46




Ruwa Hafsi ta diba a wata roba taje falo ta kwance dankwalin kanta ta jika shi tana goge masa jiki. Nafisa taje tana bude buden dakuna har taga kayan junaid. Riga kawai ta saka masa suka fice. Ihun Tilly suka ji tana kada ku barni da muzurun nan. Sai da drebansu ya sha wahala kafin ya iya kulle muzurun a kitchn dama ta taga ya shiga. Bakin Tilly duk jini don ta sha faratansa masu tsini suka tausaya mata ta shiga motar tare dasu. Asibitin kudi suka je inda aka yiwa junaid gwaje gwaje likita ya tabbatar babu abinda ke damunsa sai yawan tunani da bacin rai. Mummy da senator ma sun zo ana yiwa Tilly dressing din ciwukanta. Babu wanda ya kula ta a cikinsu suka wuce wurin Junaid.

Washegari sai wurin shadaya na safe Junaid ya farka. Koda ya bude idanu iyayensa ya gani da yan uwansa. Hajiyan dangi ma tazo daga kano. Yunkurin tashi yayi yaji hannu ya danne shi ta baya Juni ka kwanta jikinka ba kwari fa. Na shiga uku ce ta subutu daga bakinsa. Don har zuciyarsa saida ta kada don yanzu tilly tsoro take bashi. Yace me kike a nan ba na sake ki ba? Wani murmushi mummy tayi har kana ganin hakoranta, ita kuwa Tilly me kumburarriyar fuska tace dont mind him zafin ciwo ne yake damunsa. Imran da yake asibitin tun safe bayan ya kira wayar hamida ta dauka yace ke bana son iskanci...sai yayi saurin rufe bakinsa Allah na tuba. A gabana yayi mata saki uku wallahi kuma harda text ma shaida. Karya yake Mummy don Allah kada ku rabani da Juni. Nafisa tace idan ma joni ne ke da shi har abada. Kuma idan baki fita ba Allah security zan kira miki. Ta kalli su Hajiya tace ai a kwance muka ganta tana wani tsafi muzuru na lasheta kamar maye. Duk shi yaji mata ciwo. Tilly cikin kuka da daga murya tace wallahi karya ne bana tsafi. A jikin Juni nayi niyar shafa maganin shine na fadi ya goge a jikin mage. Subhanallahi dama asirce shi kike yi. Saurin rufe bakinta tayi jin baram baramar da tayi. Tana girgiza hannayenta da kanta tace ba haka nake nufi ba wallahi. Hamida ce ta bude kofa zata tura Tilly waje sai ga muzuru ya shigo ji kake yana meooowww da yaga Tilly. Bayansa nurses biyu ne da wani cikin masu gadi sun biyoshi da gudu. Jikin Tilly ya dafe yana zazzare idanu harda wani lafewa a kafadarta. Ita dai mutuwar tsaye tayi ko motsi ta kasa. Maigadin yace kuyi hakuri muna binsa yana gudu kamar yasan inda zashi ne. Imran dariya har kasa ta kaishi yace no ka barshi kawai ga matarsa nan ya nuna Tilly dake hawaye ba kakkautawa. Tausayi ta bawa hajiya tace don Allah a raba ta dashi. To dai jikin Tilly kamar me wasan kura da kyar aka rabasu don sai da aka yiwa muzurun allurar bacci ya fado. Tana ta godiya nan ta fada musu duk sharrin data kulla ita da Rosie ta roki gafarar su. Hafsi da ke can gefe akan kujera Tilly ta kalla tace kema sharrin dana yi miki babu ma cikin kawai so nayi ya sake ki.

Nan dai kowa yace ya yafe Nafisa tace ina kudin da kika karba wurin Junaid. Sai lokacin ma ta tuna cikin kankanuwar murya tace yana drawer a gida. Nafisa ta sha kunu to babu ke babu su don har atm din Alhajinmu ya sata yana baki kudi. Daga nan ki san inda dare yayi miki.

Hajiya tace to kuzo mu tafi gida don a kawo musu abinci. Hafsi ce kan gaba Hajiya tace ni bana son gulma zauna wurin mijinki kinji ko. Kamar tayi kuka duk suka fice. A bakin kofar ta tsaya taki juyuwa ma ta kalleshi. Kusan minti goma tayi a haka har kafaŕta ta fara sagewa shi kuwa Junaid dama kyaleta yayi don yaga iya gudun ruwanta. Yana kallonta ta sa nauyi a wannan kafar idan ta gaji ta canja. Murmushi tayi don ta fara bashi tausayi.




Batul Mamman💖

Post a Comment (0)