TUN KAFIN AURE 48

TUN KAFIN AURE💐48




A tsorace ta shiga compound din da dakin Rosie yake cike da zulumi. Bata san da idon  da zata kalli kawar tata ba bayan irin sakayyar da tayi mata ta mugunta. Yan matan gidan masu zaman banza ne suke binta da ido lokacin da ta shigo gidan. Ai dole su kalleta fuskarta har ta canja kama. Gata kai babu ko dan kwali yar hular gashin data saka ma tuni muzuru ya tuge. Kofar dakin ta kama zata bude taji a rufe ta fara bugu iya karfinta. Rosie don Allah ki bude nice. Nasan ban kyauta miki ba amma don Allah ki yafe min. Tambai mai gidan ce ta fito tare da sauran matan duk suna ta kallonta Tambai ta koma daki ta dauko wani abu cikin katon mayafinta ta mikawa Tilly tare da wata takarda. Kiyi hankuri fa kawarki ta mutu kwana biyu da sunka shige. Wani ihu ta fasa tare da yin zaman dirshan a kasa. Ta bude zanin baby ne yake bacci. Kuka take iyakar karfinta Rosie ki yafe min wayyo Allah na mun tuba. Allah Ka yafe mana. Ta kankame jaririn Tambai da sauran mata suna bata hakuri. Sai da ta gaji don kanta ta mike tace yaushe ta rasu. Wata mata tace mata yau kwana biyu kenan. Yunwa ce ta kasheta ga nakuda ta wahala kafin ta haihu. Wata kuma tace ke baki da imani ba kece kika auri dan sanata ba amma ko sau daya baki zo ba. Haka suka gama cece kucensun kowacce ta koma dakinta. Tambai ta mika mata mukulli tace ki kwashe kaya don kudin haya ya kare. Tana bude dakin wasu hawaye masu zafi suna saukar mata. Ta kalli baby din da ya kura mata ido tace ka yafe min dana na kashe maka mahaifiya amma daga yau nice mamanka. Sunana na gaskiya bama talatu bane sunana Safiya. Ta bude takardar tana karatu tana kuka.
                           1/1/20..

Assalam alaikum Talatu, idan kin sami takardar nan to hakika rai yayi halinsa.  Ya yar uwata munyi rayuwa tamkar tumaki marasa alkibla. Nice ma sanadiyar lalacewarki bayan kin baro gidanku a dalilin fyade da kanin babanki yayi miki aka karyata ki. Nima wahala ce ta kawoni ga wannan rayuwar a dalilin maraici kamar yadda kika sani. Sai dai kuma duk tsananin rayuwa ba hujja bace ta iskanci. Nayi nadama mara iyaka kuma naje wurin malam ya warware abinda aka yiwa Junaid. Ki rokeshi da duk wanda kika san muamala ta hada mu ya yafe min. Kema ki tuba don Allah.

Hawaye ta share tace na tuba nima nabi Allah da manzonSa.

Ga abinda Allah Ya bani nasan dai aikin da wahala ki taimaka ki bashi tarbiyar da mu bamu samu ba. Ki koya masa tsoron Allah da azabarSa. Na saka masa suna Abdallah bawan Allah. Allah Yasa muna da rabon rahmarsa.
Ashhadu an lailaha illallah wa ashhadu anna muhammadar rasulullah.
                 Yar uwarki
          Samira Jafaru.

Nima a gefe saida nayi hawaye. Talatu au na manta Safiya ta rungume Abdallah tana ta kuka. Allah Ya gafarta miki Samira Allah Ya jikanki. Haka ta zauna tayi yan kwanaki har dan abin hannunta ya kare. Ga Abdallah ba abinci. Karfe tara na dare Tambai tasa samari suka yi boli da Safiya da kayansu. Babu abinda ta dauka sai kayan jikinsu ta goya Abdallah suka fita daga gidan. Yanzu ina na nufa ta fada a zuciyarta.




Batul Mamman💖



Post a Comment (0)