TAMBAYA TA 014


*RAMUWAR AZUMIN FARILLA A SHARI'A*

Salam shin ya alatta mutum ya ringa skiping yayin yin rankon azummi? Misali kana yinshi litinin da alhamis kuma ranko ne.

AMSA

Wa'alaikumussalaam Wa Rahmatullahi Wa Barakaatuh.
Babu laifi akan hakan shine abin da mafi yawancin mallamai suka tafi a kai wanda yake da ramuwa na azumin Ramadan yayin da zai rama su, ba dole sai ya yi su a jere ba, saboda fadin Allah(SWT):

(فمن كان منكم مريضا أو على سفر فعدة من أيام أخر)

Wanda ya kasance daga cikin ku bashi da lafiya ko a hali na tafiya to sai ya biya adadin a cikin wasu kwanuka na dabam.

-Haka an ruwaito daga Aisha Allah Ya kara mata yadda tace da an saukar da àyar

(فعدة من أيام أخر متتابعات)

Sai aka goge kalmar (متتابعات)

-Haka an ruwaito hadisi daga Abdullahi binu Umar (RTA) Ya ce manzon Allah(SAW) yace:
(أن النبي صلى الله عليه وسلم قال في قضاء رمضان إن شاء فرق وإن تابع)سنن الدارقطني.

Manzon Allah(SAW) ya ce: Wanda yake da ramuwa na azumi idan ya so ya yi su a jere idan ya so ya yi su a rarrabe.
والله تعالى أعلم.

DR, NASIR YAHYA ABUBAKAR BIRNIN GWARI

03-FEB-2020


Daga
*MIFTAHUL ILMI*

 ```Ga masu sha'awar Shiga Zauren MIFTAHUL ILMI WhatsApp sai a aiko da cikakken suna ta WhatsApp zuwa ga lambar Mu 07036073248```
Post a Comment (0)