HALAYEN MUTANE BAYAN RAMADAN


*Halayen Mutane Bayan Ramadan*
🌹🌹🌹🌹🌹🌹

Halayen mutane a bayan Ramadan ya kasu kashi 4.

👉🏻 *Kaso na farko*
Sune wadanda ta sanadiyyar watan Ramadan Imanin su ya karu, suka kara kusanci da mahaliccinsu, suka lizimci aikin da'a tareda kokari wajen nesantar aikin laifuka...... *Madallah da wanda ya fada a wannan kaso*👌🏻

👉🏻 *Kaso na biyu* 
Sune wadanda bayan Ramadan suka koma ruwa wajen lizimtar manyan ayyukan laifuka bayan a cikin Ramadana kuma sun kame basu aikatawa..... *Wadannan sun zama masu bautar Ramadana, Allah ya tsaremu*🤦🏻‍♂

👉🏻 *Kaso na uku*
Sune wadanda suke tsaka tsakiya a bayan watan Ramadana, wani lokacin su aikata ayyukan alkhairan da suka saba aikatawa a watan, wani lokacin kuma sai shaidan ya rinjayesu........ *Tsira da kubutarwa su tabbata ga wannan kaso*🙏🏻

👉🏻 *Kaso na Hudu*
Wadannan sune kaso na karshe wadanda daman basuci ribar watan Ramadana ba haka nan ma bazasuci riba bayansa ba, daman yayi dai dai da fadar Manzon Allah (SAW) da yake cewa: *"da yawa wasu masu azumi basuda ladar azumi sai dai yunwa da kishiri ruwa"*....... *wannan kaso sun tabe kuma sunyi hasara*🙆🏻‍♂

Muna addu'a Allah yasa yadda muka jajirce wajen bautama Allah a cikin Ramadan yasa mu kara jajircewa a bayansa👏🏻
➖➖➖➖➖➖
Domin neman karin bayani kuyi downloading wannan Littafin dake a kasa mai suna *"ماذا بعد رمضان؟"*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
https://t.me/ansarussunnah
Post a Comment (0)