MATSAYIN ZAKKA A SHARI'ANCE 4


_*⚖️MATSAYIN ZAKKA A' SHARI'ANCE⚖️*_(4)

LOKACIN DA AKA WAJABTA TA:
DAKUMA KUMA WADANDA TA WAJABA AKANSU!!

 Malamai sun yi sabani game da lokacin da aka wajabta Zakka.

 Wadansu sun ce an wajabta ta ne a Makka.
 Saboda ayoyin Makka wadanda suka yi magana a kanta. 

Wasu kuma suka ce an wajabta ta ne a Madina. 
Saboda ayoyin Madina sun fi bayyana wajabcin ta.

 masu Magana ta biyu sun fi kawo hujja mai Karfi. 
Inda suka ce musulmi a Makka daidaiku ne. 
Basu da tsari zartacce. 
Ba su da hukuma. 
Ita kanta Zakkar ma ba ta da tsari wannan lokacin. 

Watau ba ta da nisabi. 
Ba a kuma ayyana wadanda za a bai wa ba. 
Don haka maganar da ta fi rinjaye ita ce, an wajabta Zakka ne a Madina, 
a shekara ta biyu bayan Hijira. 

(Duba fiKhuz Zakkat na 
Dr. Yusuful Kardawi, 
Juz’I na 1 sh:52-62.)

WADANDA TA WAJABA A KAN SU:

 Malamai sun hadu a kan cewa Zakka tana wajaba a kan Musulmi, baligi, mai hankali. Kuma wanda ya mallaki nisabi, tare da cika sauran sharuda. 

Amma sun yi sabani a kan yaro da mahaukaci. Wasu sun ce ba ta wajaba a kansu ba. 
Wasu kuma suka ce tana wajaba. 

Amma magana ta biyu ita tafi Karfi,

 saboda hadisai ingantattu da aiwatarwar sahabbai a kan haka.  

Dabarani ya rawaito hadisi, kamar haka;-

"عن أنس بن مالك قال: قال رسول الله صلى الله عليه وسلم، اتجروا في أموال اليتامى، لا تأكلها الزكاة.

Wato daga Anas (RA) ya ce, Manzon Allah (SAW)
ya ce: “Ku yi ciniki da dukiyar marayu, domin kada Zakka ta cinye ta”. 
(Duba FiKhuz Zakkat juz’i na 1, sh:95 – 112.)

Wannan ya nuna cewa za a fitar da Zakka daga dukiyar yaro da ta mahaukaci.

_*Zamuci gaba insha Allah!!*_
Rubutawa>>✍🏼
*Abubakar Sadiq Salihu Kabara*

Gabatarwa_
_*ALHUSEIN ABBAN SUMAYYA*_

*_Ga masu sha'awar bin shirye shiryrnmu ta Telegram se yabi ta_*👇🏽
https://t.me/miftahul_ilmi

Dan kasancewa damu ta
WhatsApp
_*Miftahul ilmi*_
Se a turo cikakken suna da Address ta wan nan Number👇🏽
07036073248
Post a Comment (0)