TAMBAYA TA 138


*MAI TAKABA ZATA IYA FITA SALLAR IDI?*


*Tambaya*

Assalamu alaikum warahmatullah, Barka da war haka. Don Allah YA halatta me takaba ta je sallar Eid?


*Amsa*
Wa alaikum assalam,

 Bai halatta ga mai takaba ba ta fita zuwa Idi, saboda Hadisin Ibnu Majah Mai lamba ta: (2031) inda Annabi SAW yake cewa da Furaia lokacin da mijinta ya Rasu: (Ki zauna a cikin gidan da kika samu labarin mutuwar mijinki har zuwa Ki kammala iddarki"
Hadisin da ya gabata yana nuna cewa: Mai takaba ba za ta fita ba sai in akwai lalura, sallar idi kuma ba ta cikin lalorori a sharia. 

Imamu Ashshaukani a cikin Nailul Audaar 3/343 ya yi bayani cewa "Dukkan Mata ana fitar da su daga gidanjansu Don su halarci idi, in ban da wacce take iddar mutuwa. 

Allah ne mafi Sani

*Dr, Jamilu Zarewa*

03/09/2017
Post a Comment (0)